ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Ainihin Halin Da Ake Ciki A Xinjiang? Mu Ji Ta Bakin Wadannan Masu Yawon Shakatawa Na Japan

by CMG Hausa
3 years ago
Xinjiang

Wasu masu yawon shakatawa 20 na kasar Japan sun yi yawo a sassan jihar Xinjiang da ke arewa maso yammacin kasar Sin cikin tsawon kwanaki 9, inda suka gane ma idanunsu yanayin rayuwar al’ummar jihar da ma al’adunsu. 

Kafin wannan, ofishin jakadancin kasar Sin da ke Japan ta shirya wani aiki na tara masu yawon shakatawa da suke son zuwa jihar Xinjiang, kuma dimbin mutanen kasar ta Japan sun yi na’am da kiran, wadanda kuma suka biya kudin yawon da kansu. Sai dai kafin su fara wannan ziyara, sun nuna shakku game da yanayin da ake ciki a jihar, sakamakon rahotannin da kafofin yada labarai na kasarsu suka bayar game da jihar.

  • Sin Ta Amince Da Yarjejeniyar Tallafin Kamun Kifi Ta WTO

Da suka isa Xinjiang, sun ziyarci gonakin auduga na zamani, inda suka samu fahimtar yadda ake amfani da na’urorin zamani wajen noman auduga, wato cikin kwanaki biyu kadai za a iya kammala shuka auduga a gonaki masu fadin eka 20, tare da kammala aikin fesa maganin noma cikin sa’o’i biyar. A game da wannan, Akihiko Inoue ya ce abin ya burge shi matuka, wanda ke nuni da cewa babu wani batu na “aikin tilas” da kafofin yada labarai na kasarsu Japan ke watsawa, saboda tuni aka fara yin amfani da na’urorin zamani wajen ayyukan gona a jihar ta Xinjiang. A wata masaka kuma, da suka ga yadda ma’aikata masu kwarin gwiwa ke amfani da injunan saka na zamani, malama Watanabe Yumi ta ce, tabbas za ta bayyana abubuwan da ta gani da idanunta ta shafinta na sada zumunta, don fahimtar da karin mutane a kan hakikanin yanayin da ake ciki a Xinjiang, saboda ya sha bamban da ikirarin keta hakkin dan Adam da kafofin yada labarai na kasarsu ke yadawa.

ADVERTISEMENT

A cikin ’yan shekarun baya, jami’an diplomasiyya da ’yan jarida sama da 1000 da suka fito daga kasashe da yankuna fiye da 100 sun ziyarci Xinjiang, inda suka gane ma idanunsu kyakkyawan yanayin jihar Xinjiang da bunkasuwarta.

Sai kuma a tarukan da majalisar hakkin dan Adam ta MDD ta shirya a shekarun baya, kusan kasashe dari suka yi ta bayyana goyon bayansu ga matsayi mai adalci na kasar Sin, tare da yin Allah wadai da kasashen yammacin duniya bisa manufar siyasa da suke neman cimmawa.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

A gaba, muna maraba da karin baki da su ziyarci jihar Xinjiang. Don Gani Ya Kori Ji. (Lubabatu)

 

Xinjiang
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Jagororin ’Yan Kasuwa Sun Bayyana Kwarin Gwiwa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Yayin Taron Davos

Jagororin ’Yan Kasuwa Sun Bayyana Kwarin Gwiwa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Yayin Taron Davos

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.