Tsohon gwamnan jihar Zamfara kuma sanata mai wakiltar Zamfara ta Yamma, Abdulaziz Yari, ya buƙaci limamai da malaman addinin Musulunci da su ƙara ƙaimi wajen yin addu’a domin samun nasara a yaƙin da ake yi da ‘yan bindiga a jihar.
Yari ya yi wannan kira ne yayin ganawarsa da limamai da malamai a gidansa da ke Talata Mafara, inda ya jaddada muhimmancin rawar da Malaman addini ke takawa wajen gyaran tarbiyya da wayar da kan al’umma.
Ya bayyana cewa malamai na da kusanci da jama’a, don haka suna taka muhimmiyar rawa wajen gina zaman lafiya da haɗin kai a cikin al’umma.
Sanatan ya kuma yi addu’ar Allah ya haɗa kai tsakanin gwamnatin jihar da ta tarayya, yana mai fatan gwamna Dauda Lawal zai samu goyon bayan da ya dace domin ƙarfafa yaƙi da ‘yan bindiga.
A ƙarshe, ya buƙaci al’ummar Zamfara da ma Nijeriya gaba ɗaya su ci gaba da addu’o’i domin samun zaman lafiya mai ɗorewa da kawo ƙarshen matsalar tsaro a ƙasar.















Discussion about this post