ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

by Sulaiman and Hussein Yero
25 seconds ago
Zamfara

Akalla dattawa 50 daga kauyen Magamin Diddi da ke yankin Magami/Faru a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara ne aka yi garkuwa da su yayin wani zaman sulhu da suka yi da fitaccen shugaban ’yan bindiga, Jammo, wanda ke iko da dajin Muntsira da ke Maradun.

Da yake zantawa da LEADERSHIP kai tsaye, shugaban karamar hukumar Maradun, Hon. Bello Dosara, ya ce dattawan kauyen sun gana da shugaban ’yan bindigar ba tare da amincewar gwamnati ba.

Ya ce, “Ni ne babban jami’in tsaro na Maradun, ya kamata su tuntuɓe ni a kalla. Babu wanda ya sanar da ni saboda sun san gwamnatin jihar Zamfara karkashin Gwamna Dauda Lawal ta haramta tattaunawa da ’yan bindiga.

ADVERTISEMENT

“Yanzu haka na karanta wani rahoto da ya ce mutum 11 ne aka saki, amma ‘yan mintuna kaɗan da suka wuce kafin kiran wayarka, an tabbatar min cewa dattawa 12 aka saki, saura 38 suna hannunsu,” in ji Dosara.

Ya kara da cewa, “Ya saki mutum 12 ɗin ne domin su je su sanar da al’umma abin da ya faru.”

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

Shi ma wani shugaban matasan al’ummar, wanda ya nemi a ɓoye sunansa, ya tabbatar wa LEADERSHIP faruwar lamarin, yana mai cewa shugaban ’yan bindigar Jammo ya kuma hana mutanen kauyen zuwa kasuwar yankin.

Ya bayyana cewa shugaban ’yan bindigar ne ya nemi a yi sulhu bayan an kashe ɗaya daga cikin yaransa a wani samamen sojoji da aka kai a kauyen Kandare kwanan nan.

Zamfara
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un
  • Sulaiman
    Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci
  • Sulaiman
    Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?
  • Sulaiman
    A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
Zamfara
Hussein Yero
+ posts Bio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Abdulaziz Yari Ya Bukaci Limamai Su Ƙara Addu’a Kan Yaƙi Da Ƴan Bindiga A Zamfara
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Matawalle Ya Buƙaci Magoya Bayansa Su Mara Wa Shugaba Tinubu, Gwamna Lawal Baya
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Majalisar Zamfara Ta Dakatar Da Shugabannin Kananan Hukumomi Biyu Kan Zargin Almundahanar Kuɗaɗe

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

June 8, 2026
Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna
Manyan Labarai

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

June 8, 2026
Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta
Manyan Labarai

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

June 8, 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

June 8, 2026
Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

June 8, 2026
Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

June 8, 2026
Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

June 8, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026
Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Tattaunawar Neman Aiki…

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Tattaunawar Neman Aiki…

June 8, 2026
Morocco Na Fargabar Rashin Ƴan Wasa 2 Gabanin Karawa Da Brazil

Morocco Na Fargabar Rashin Ƴan Wasa 2 Gabanin Karawa Da Brazil

June 8, 2026
Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

June 8, 2026
Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

June 8, 2026
Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

June 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.