Akalla dattawa 50 daga kauyen Magamin Diddi da ke yankin Magami/Faru a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara ne aka yi garkuwa da su yayin wani zaman sulhu da suka yi da fitaccen shugaban ’yan bindiga, Jammo, wanda ke iko da dajin Muntsira da ke Maradun.
Da yake zantawa da LEADERSHIP kai tsaye, shugaban karamar hukumar Maradun, Hon. Bello Dosara, ya ce dattawan kauyen sun gana da shugaban ’yan bindigar ba tare da amincewar gwamnati ba.
Ya ce, “Ni ne babban jami’in tsaro na Maradun, ya kamata su tuntuɓe ni a kalla. Babu wanda ya sanar da ni saboda sun san gwamnatin jihar Zamfara karkashin Gwamna Dauda Lawal ta haramta tattaunawa da ’yan bindiga.
“Yanzu haka na karanta wani rahoto da ya ce mutum 11 ne aka saki, amma ‘yan mintuna kaɗan da suka wuce kafin kiran wayarka, an tabbatar min cewa dattawa 12 aka saki, saura 38 suna hannunsu,” in ji Dosara.
Ya kara da cewa, “Ya saki mutum 12 ɗin ne domin su je su sanar da al’umma abin da ya faru.”
Shi ma wani shugaban matasan al’ummar, wanda ya nemi a ɓoye sunansa, ya tabbatar wa LEADERSHIP faruwar lamarin, yana mai cewa shugaban ’yan bindigar Jammo ya kuma hana mutanen kauyen zuwa kasuwar yankin.
Ya bayyana cewa shugaban ’yan bindigar ne ya nemi a yi sulhu bayan an kashe ɗaya daga cikin yaransa a wani samamen sojoji da aka kai a kauyen Kandare kwanan nan.














Discussion about this post