Ɗan takarar Sanatan Zamfara ta Arewa a jam’iyyar APC, Sani Abdullahi Shinkafi, ya bayyana cewa rayuwarsa na cikin haɗari, kan zargin wasu da ƙoƙarin hana shi tsayawa takara a zaɓen 2027.
Shinkafi ya bayyana haka ne yayin ganawa da manema labarai a Gusau, babban birnin Jihar Zamfara.
Ya ce akwai mutanen da suke son kashe shi saboda alaƙarsa da Abdul’aziz Yari da wasu manyan ’yan siyasa, da kuma burinsa na tsayawa takarar Sanata.
Ya kuma ce gayyatar da hukumar EFCC ta yi masa kan wasu kuɗaɗe da suka shiga asusun kamfaninsa na daga cikin ƙoƙarin hana shi tsayawa takara.
A cewarsa, ana zarginsa da karɓar kuɗaɗen ne domin ɗaukar nauyin ta’addanci, amma ya ce ba zai janye daga takarar ba.
Shinkafi ya ƙara da cewa mutanen mazaɓarsa ne suke son ya tsaya takara saboda suna buƙatar shugabanci na gaskiya da kula da jama’a.















Discussion about this post