An yi jana’izar wasu daga cikin jami’an Rundunar Sojojin Nijeriya da aka kashe, ciki har da marigayi Birgediya Janar Omo Braimo, Kyaftin Ismail, da sauran sojoji da suka rasu a yayin yaki da ‘yan ta’adda, a ranar Laraba tare da cikakken girmamawar soja a makabartar Maimalari Cantonment da ke Maiduguri, Jihar Borno.

Wannan taron jana’iza mai cike da jimami ya haɗa manyan jami’an gwamnati, manyan hafsoshin sojoji, iyalai masu alhini, da abokan aiki, domin karrama jaruman da suka sadaukar da rayuwarsu wajen yi wa ƙasa hidima.

Daga cikin waɗanda suka halarta akwai gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum; Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya); Babban Hafsan Tsaro, Janar Olufemi Oluyede; Babban Hafsan Sojojin Ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu; da Sanatan Borno ta Kudu, Mohammed Ali Ndume.
A cikin jawaban ta’aziyyarsu, manyan baƙin sun bayyana mamatan a matsayin jarumai masu kishin ƙasa, waɗanda suka tsaya tsayin daka duk da haɗarin da suka fuskanta.














Discussion about this post