A jiya Juma’a, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gana da manyan jami’an dimbin kasashe, yayin da yake halartar taron tattauna harkar tsaro na Munich a kasar Jamus.
Lokacin da yake ganawa da sakataren harkokin wajen kasar Amurka Marco Rubio, Wang Yi ya ce, kamata ya yi, bangarorin Sin da Amurka su yi kokarin aiwatar da ra’ayi daya da shugabannin kasashen 2 suka cimma, da mai da shekarar 2026 ta kasance shekarar da kasashen Sin da Amurka suke mutunta juna, da zama cikin lumana, gami da hadin kai don tabbatar da moriyar juna. Kana a yayin ganawarsu, jami’an 2 na Sin da Amurka sun yarda da amfani da matakan diflomasiyya wajen daidaita harkoki, da kara kyautata huldar dake tsakanin kasashensu.
Ban da haka, duk a gefen taron tattauna batun tsaro na Munich, Wang Yi, da ministan wajen kasar Jamus, Johann Wadephul, da takwaransu na kasar Faransa, Jean-Noel Barrot, sun yi ganawa ta bangarori 3, inda Mista Wang ya ce, ci gaban kasar Sin dama ce ga kasashen Turai, kana kalubalolin da nahiyar Turai ke fuskanta ba daga kasar Sin ake samunsu ba. Saboda haka jami’in ya ce kasar Sin na son ganin kasashen Jamus da Faransa sun taimaka wajen daidaita ra’ayin kasashen Turai kan kasar Sin, da tsayawa kan raya huldar abota tsakanin Sin da Turai. Yayin ganawarsu, dukkan jami’an 3 sun bayyana haduwar wannan karo a matsayin mai matukar ma’ana, kana sun amince da ci gaba da musayar ra’ayi kan manyan tsare-tsaren kasashensu.
Ban da haka, Wang Yi ya gana da shugaban Serbia Aleksandar Vucic, gami da ministocin waje na kasashen Birtaniya, da Austria, da Argentina, da kuma Ukraine. (Bello Wang)















Discussion about this post