Ministar harkokin wajen kasar Madagascar Christine Razanamahasoa ta bayyana a ranar Asabar cewa, ana fatan za a inganta alakar dake tsakanin Madagascar da kasar Sin zuwa sabon matsayi, kana ta mika gaisuwa ga jama’ar kasar Sin a yayin maraba da zuwa Bikin Bazara na Sinawa.
Minista Razanamahasoa ta bayyana a yayin bikin liyafar cin abincin Sinawa domin murnar Bikin Bazara na kasar Sin wanda ofishin jakadancin Sin dake kasar Madagascar ya gudanar cewa, a sabuwar shekara, kasar Madagascar tana son kara yin imani da juna, da zurfafa hadin gwiwar tattalin arziki da zuba jari, da sa kaimi ga yin mu’amalar al’adu tare da kasar Sin don neman cimma burin raya al’umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan bil’adama.
Hakazalika, Razanamahasoa ta bayyana cewa, kasar Madagascar da kasar Sin sun kiyaye raya dangantakar abokantaka a dogon lokaci, tana son raya dangantakar din zuwa sabon mataki, da zurfafa hadin gwiwar tattalin arziki a tsakaninsu don amfanar da jama’arsu baki daya. (Zainab Zhang)















Discussion about this post