ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ramadan: Gwamna Uba Sani Ya Yi Kira Ga Malamai Da Su Ƙarfafa Haɗin Kai

by Shehu Yahaya and Sulaiman
4 months ago
Ramadan

Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Uba Sani, ya bukaci malamai na addinin Musulunci da kafafen yaɗa labarai tare da kafafen sadarwar zamani da su yi amfani da watan Ramadan mai zuwa a matsayin wata babbar dama ta ƙarfafa zaman lafiya, haƙuri da haɗin kan ƙasa.

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a wajen taron Shekara-shekara na Kafin Ramadan na 2026 da Jama’atu Nasril Islam (JNI) ta shirya a Babban Hedkwatarta da ke Kaduna.

ADVERTISEMENT
  • CBN Ta Amince Wa Bankin Masana’antu Buɗe Sashin Bankin Da Babu Riba
  • Dalilin Da Ya Sa Gwamnan Bauchi Ya Sauke Kwamishinan Tsaron Cikin Gida

Gwamna Uba Sani, wanda Sakataran Gwamnatin Jihar Kaduna, Dakta Mu’azu Meyare, ya wakilta, ya jaddada cewa matsalolin tattalin arziƙi, tsaro da zamantakewa da ƙasar ke fuskanta a halin yanzu sun ƙara ɗora nauyi a wuyan malamai da kafafen yaɗa labarai wajen jagorantar al’umma da hikima, ladabi da tausayi.

 

LABARAI MASU NASABA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

Akan hakan , Gwamnan ya yi kira ga malamai da su tabbatar da cewa darussan tafsiri da sauran shirye-shiryen wayar da kai na ramadan suna ƙarfafa haɗin kai, zaman lafiya, adalcin zamantakewa da kula da marasa galihu.

 

Ya bayyana cewa watan ramadan, wata ne mai tsarki da rahama, tarbiyya inda ya bukaci al’umma da suyu amfani da watan wajen ƙarfafa dabi’un sadaka, kishin ƙasa da addu’o’i ga ƙasa da shugabanninta.

 

Ya ƙara da cewa addu’o’i na gaskiya a wannan wata mai albarka suna da muhimmiyar rawa wajen warkar da ƙasa.

 

Gwamnan ya kuma yi kira ga gidajen rediyo, talabijin da kafafen sada zumunta na zamani da su kiyaye ƙa’idojin ƙwarewa da ladabi wajen watsa tafsiri da sauran shirye-shiryen addini, yana mai gargadin cewa a guji saƙonnin da ka iya tayar da fitina ko rarrabuwar kai.

 

Ya kumq tunatar da mahalarta cewa yi wa bil’adama hidima na daga cikin manyan ibadu a Musulunci.yana mai bayyana jajircewar Gwamnatin Jihar Kaduna ga shugabanci mai haɗa kowa da kowa, Gwamnan ya ce tsarin haɗin kai tsakanin addinai da gwamnati ta kafa ya taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya da fahimtar juna a tsakanin mabambantan addinai.

 

Hakazalika, ya tabbatar da goyon bayan gwamnati ga ilimin addini da tattaunawa, tare da yin alƙawarin ci gaba da haɗin gwiwa da JNI da sauran ƙungiyoyin addini.

 

Gwamnatin Jihar Kaduna ta sake jaddada shirinta na yin aiki kafada da kafada da malamai da kafafen yaɗa labarai domin zurfafa haƙuri, ƙarfafa haɗin kai da tabbatar da watan Ramadan mai cike da zaman lafiya da albarkar ruhi.

 

 

Taron ya gudana ne ƙarƙashin jagorancin Mai Martaba Shehun Borno, Alhaji Dakta Abubakar Ibn Umar Garba Abba Kiyari El-Kanemi, wanda ya jagoranci tattaunawar da ta mayar da hankali kan wa’azi mai alhaki, jituwa ta addini da kare zaman lafiya a lokacin Ramadan da bayan sa.

 

Taron Kafin Ramadan na JNI ya samu halartar manyan mutane daga sassa daban-daban na ƙasar, ciki har da sarakunan gargajiya, fitattun malamai da shugabannin al’umma, lamarin da ya nuna muhimmancin taron a matakin ƙasa wajen tsara tafarkin wa’azi da koyarwar addini gabanin watan Ramadan.

Ramadan
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Bayan Shehu Sani Ya Ƙalubalanci Zailani, Rikicin APC Ya Ƙara Zafi A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ya Dace ‘Yan Arewa Su Ƙara Marawa Tinubu Baya Domin Kammala Wa’adi Na Biyu — Shehu Sani
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Zargin Ware Ɓangaren El-rufa’i: Rikicin Cikin Gida Ya Kaure A Jam’iyyar ADC, Kaduna
Ramadan
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Yi Rangadin Ayyukan Kirkire-Kirkiren Kimiyya Da Fasaha A Beijing

Xi Jinping Ya Yi Rangadin Ayyukan Kirkire-Kirkiren Kimiyya Da Fasaha A Beijing

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.