ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ramadan: Gwamna Uba Sani Ya Yi Kira Ga Malamai Da Su Ƙarfafa Haɗin Kai

by Shehu Yahaya and Sulaiman
4 months ago
Ramadan

Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Uba Sani, ya bukaci malamai na addinin Musulunci da kafafen yaɗa labarai tare da kafafen sadarwar zamani da su yi amfani da watan Ramadan mai zuwa a matsayin wata babbar dama ta ƙarfafa zaman lafiya, haƙuri da haɗin kan ƙasa.

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a wajen taron Shekara-shekara na Kafin Ramadan na 2026 da Jama’atu Nasril Islam (JNI) ta shirya a Babban Hedkwatarta da ke Kaduna.

ADVERTISEMENT
  • CBN Ta Amince Wa Bankin Masana’antu Buɗe Sashin Bankin Da Babu Riba
  • Dalilin Da Ya Sa Gwamnan Bauchi Ya Sauke Kwamishinan Tsaron Cikin Gida

Gwamna Uba Sani, wanda Sakataran Gwamnatin Jihar Kaduna, Dakta Mu’azu Meyare, ya wakilta, ya jaddada cewa matsalolin tattalin arziƙi, tsaro da zamantakewa da ƙasar ke fuskanta a halin yanzu sun ƙara ɗora nauyi a wuyan malamai da kafafen yaɗa labarai wajen jagorantar al’umma da hikima, ladabi da tausayi.

 

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

Akan hakan , Gwamnan ya yi kira ga malamai da su tabbatar da cewa darussan tafsiri da sauran shirye-shiryen wayar da kai na ramadan suna ƙarfafa haɗin kai, zaman lafiya, adalcin zamantakewa da kula da marasa galihu.

 

Ya bayyana cewa watan ramadan, wata ne mai tsarki da rahama, tarbiyya inda ya bukaci al’umma da suyu amfani da watan wajen ƙarfafa dabi’un sadaka, kishin ƙasa da addu’o’i ga ƙasa da shugabanninta.

 

Ya ƙara da cewa addu’o’i na gaskiya a wannan wata mai albarka suna da muhimmiyar rawa wajen warkar da ƙasa.

 

Gwamnan ya kuma yi kira ga gidajen rediyo, talabijin da kafafen sada zumunta na zamani da su kiyaye ƙa’idojin ƙwarewa da ladabi wajen watsa tafsiri da sauran shirye-shiryen addini, yana mai gargadin cewa a guji saƙonnin da ka iya tayar da fitina ko rarrabuwar kai.

 

Ya kumq tunatar da mahalarta cewa yi wa bil’adama hidima na daga cikin manyan ibadu a Musulunci.yana mai bayyana jajircewar Gwamnatin Jihar Kaduna ga shugabanci mai haɗa kowa da kowa, Gwamnan ya ce tsarin haɗin kai tsakanin addinai da gwamnati ta kafa ya taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya da fahimtar juna a tsakanin mabambantan addinai.

 

Hakazalika, ya tabbatar da goyon bayan gwamnati ga ilimin addini da tattaunawa, tare da yin alƙawarin ci gaba da haɗin gwiwa da JNI da sauran ƙungiyoyin addini.

 

Gwamnatin Jihar Kaduna ta sake jaddada shirinta na yin aiki kafada da kafada da malamai da kafafen yaɗa labarai domin zurfafa haƙuri, ƙarfafa haɗin kai da tabbatar da watan Ramadan mai cike da zaman lafiya da albarkar ruhi.

 

 

Taron ya gudana ne ƙarƙashin jagorancin Mai Martaba Shehun Borno, Alhaji Dakta Abubakar Ibn Umar Garba Abba Kiyari El-Kanemi, wanda ya jagoranci tattaunawar da ta mayar da hankali kan wa’azi mai alhaki, jituwa ta addini da kare zaman lafiya a lokacin Ramadan da bayan sa.

 

Taron Kafin Ramadan na JNI ya samu halartar manyan mutane daga sassa daban-daban na ƙasar, ciki har da sarakunan gargajiya, fitattun malamai da shugabannin al’umma, lamarin da ya nuna muhimmancin taron a matakin ƙasa wajen tsara tafarkin wa’azi da koyarwar addini gabanin watan Ramadan.

Ramadan
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Ramadan
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Maniyyatan Nijeriya
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
'Yan Bindiga
Manyan Labarai

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Yi Rangadin Ayyukan Kirkire-Kirkiren Kimiyya Da Fasaha A Beijing

Xi Jinping Ya Yi Rangadin Ayyukan Kirkire-Kirkiren Kimiyya Da Fasaha A Beijing

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.