Mujallar Qiushi fitowa ta 7 da za a fitar a ranar 1 ga watan Afrilu, za ta kunshi muhimmin sharhin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya rubuta, mai taken “Kafawa da kuma aiwatar da ingantaccen ra’ayi game da samun nasarori a ayyukan jam’iyyar kwaminis ta Sin wato JKS”. Wannan wani sashi ne na muhimman maganganun Xi daga watan Disamba na shekara ta 2012 zuwa Fabrairu na shekara ta 2026.
Sharhin ya jaddada cewa, batun ra’ayi game da samun nasarori wajen gudanar da ayyukan JKS, wani batu ne mai tushe dangane da ra’ayin mayar da jama’a a gaban komai yayin da ake gudanar da harkokin jam’iyya. Dole ne ‘yan jam’iyyar JKS su nace ga bautawa jama’a bisa iyakacin kokarinsu, a matsayin babbar nasarar da suke samu a ayyukansu.
Labarin ya jaddada cewa, samun ci gaba mai inganci, babban aiki ne na farko a fannin zamanintar da al’ummar Sinawa baki daya, kuma tabbatar da samun ingantattun ci gaba, ya kamata ya zama muhimmin bangare na tantance nasarorin shugabanni da jami’ai.
Labarin ya nuna cewa, bana ita ce shekarar farko ta fara aiwatar da shirin raya tattalin arziki da zamantakewar al’ummar Sin na shakaru biyar-biyar karo na 15, kuma za a sauya jagororin shugabannin a matakai daban-daban a yankuna. Yana da matukar muhimmanci, kuma wajibi ne a yi amfani da horaswa don inganta shugabanni, da jami’ai a matakai daban-daban, ta yadda za su kafa, da kuma aiwatar da ingantaccen ra’ayi na samun nasarori a ayyukansu. (Amina Xu)















Discussion about this post