ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Munakisar Dauke Sassan CBN Da FAAN Daga Abuja Zuwa Legas…

by Bello Hamza
2 years ago
CBN

Gammayyar manyan kungiyoyin arewa da suka hada da Kungiyar Dattawa Arewa ta NEF da Kungiyar Tuntuba ta Arewa ta ACF sun nuna rashin amincewarsu da shirin Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu na mayar da wasu sassan Babban Bankin Nijeriya (CBN) da kuma Hukumar Kula Filayen Jiragen Saman Nijeriya (FAAN) daga Abuja zuwa Legas.

Al’ummar yankin arewa da dama sun yi tir da wannan shirin, inda suke cewa, ana neman cimma wata manufa ce ta durkusar da tattalin arzikin arewa a kaikaice.

  • Gwamnatin Zamfara Zata Raba Dabbobi Kyauta Ga Mata
  • AFCON 2023: An Fitar Da Jadawalin Zagaye Na 16

Da yake mayar da martani kan lamarin a cikin shirin Talabijin na intanet na LEADERSHIP, Barka da Hantsi Nijeriya da ake gabatarwa a duk ranakun aiki, da misalign karfe 9 na safe, mai magana da yawun kungiyar NEF, Kwamrade Abdul-Azeez Sulaiman, ya ce ba kawai sun yi watsi da wannan yunkurin ba ne, abu ne da za su yi tsayin daka a kai har sai sun ga abin da ya ture wa buzu nadi.

ADVERTISEMENT

“A halin yanzu kawunan al’ummar arewa a hade yake a kan kare muradunta, za a iya fahimtar haka idan aka lura da cewa, a halin yanzu kungiyar sanatocin arewa sun shiga wannan maganar har sun nemi ganawa da Shugaban Kasa Tinubu don dakile shirin mayar da wadannan ma’aikatu Legas.

“Hujjar cunkoso da ake bayarwa na mayar da wadannna sassan ma’aikatu ba karbabbe ba ne, musamman ganin ai cukoson Legas ne ya haifar da samar da Abuja a matsayin sabon babbar birinin tarayya, Abuja kuma na da issassun filayen da za a yin kowanne irin gini don samar da mafita ga ikirarin cunkoso da suke yi.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

“Wata makarkashiya ce daga yankin kudu maso yammacin kasar nan na mayar da al’ummarmu baya, musamman mata masu aiki a wadannan wuraren, mun samu labarin a halin yanzu da dama daga cikin su sun mika takadun neman barin aiki don ba za su iya barin iyalansu su koma Legas da sunan aiki ba,” in ji shi.”

Ya kuma bayyana cewa, babbar matsalar da yankin arewa ke fuskanta a halin yanzu ita ce rashin shubagani masu kishin yankin, domin shugabanin da ake da su a wanna zangon ba muradun arewa ke a gabansu ba, tara abin duniya ne kawai a gaban su, ba kamar shugabanni irin su marigayi Sir Ahmadu Bello Firimiyan farko na yankin arewa ba. “Abubuwan da shugabanin farko suka samar wa arewa don ci gaban al’umma duk an lalata su, kamar Bankin Arewa da sauran su” In ji shi

Ya kuma nemi al’ummar arewa su dunkule wuri daya ba tare da nuna bambanci kabila ko addini ba, ‘’ta haka za mu dawo da martabar al’ummarmu da kuma tabbatar da ci gaban yankinmu” in ji shi.

Daga karshe ya nemi al’ummar yankin arewa su bayar da dukkan gudummawar da ake bukata don yaki da mastalar tsaro da ke neman durkusar da yankin.

A nata bangaren kuwa, Kungiyar ACF ta bayyana cewa, shawarar CBN ta mayar da wasu sassa zuwa Legas ba an yi ba ce saboda ci gaban Nijeriya da kuma kishin kasa ko kuma domin warware wasu matsalolin da aka kasa warwarewa, sai dai don a cutar da al’ummar arewa da wasu sassan Nijeriya.

A takardar sanawar da kungiyar ACF ta fitar wanda ke dauke da sa hannun sakataren watsa labarunta na kasa, Farfesa T. A. Muhammad-Baba, ta ce, suna kallon wannan shiri a mastsyin wani kokari na ware arewa daga shiga harkokin tattalin arzikin kasa da kuma mayar da al’ummar arewa baya, ta kuma kara da cewa, ta samu wani bayanin sirri na wata wasika da wani kamfani mai suna ARFF ya rubuta wa ministan sufurin jiragen sama inda yake neman a dauke wani aiki da aka tsara yi a tashar jiragen sama na Katsina zuwa kudancin kasar nan ko kuma Abuja. Takardar ta kuma bayar da shawarar a mayar da aikin zuwa Legas, Ibadan ko Inugu.

“Yana da sauki a yi watsi da wannan shirye-shiryen na mayar da wasu ma’aikatu zuwa kudancin Nijeriya da CBN da FAAN suka fara, amma dole mu kalli shirin a matsayin shiryayyen lamari na ware yankin arewa, ko kuma ya zama wani sabon ajanda ne na mayar da al’ummarmu baya. A lokacin mulkinsa karo na farko a 1999, tsohon shugaban kasa Obasanjo ya umarci mayar da Hukumar Kula da Tashoshin Jiraghen Ruwan Nijeriya (NPA) da Hukumar Kula da Harkokin Kasashen Waje (NIIA) daga Abuja zuwa Legas.

“A yau kusan dukkan hukumomin da suka shafi teku suna garin Legas duk da cewa, a kwai wasu sassan kasa da za su iya daukar masaukin wadannan ma’aikatu.”

Sanarwa ta kuma ce, nasarar da aka samu ta gano man fetur a yankin kogin Kolmani na Jihar Gombe ya karyata masu ikiirarin cewa, babu man fetur a yankin arewa.

“Wadanna hujjojin sun sanya kungiyar ACF ba ta yarda da shirin mayar da wasu hukumomin gwamnati zuwa Legas ba”.

A kan haka ACF ta yi kira na musamman ga gwamnatin tarayya da majalisar kasa da kuma dukkan hukumomin da suke da hannu a wanna Shirin da su janye , su kuma dauki dukkan mataksn da suka kamata na kawo karshen cunkoson da suke fakewa da shi, baya ga haka ma akwai issassun filaye a Abuja da za a iya gina duk abin da ake bukata don ci gaban kasa.

“Kungiyar ACF na tunatar da al’umma cewa, fiye da shekara 20 da suka wuce aka dawo da mazaunin birinin tarayya Abuja ta hanyar doka kuma wannan dokar tana nan  har zuwa yanzu, duk da cewa, wasu da dama ba su ji dadin haka ba,” in ji sanarwar.

Jim kadan dai bayan fitar da sanarwar hukumar gudanarwar CBN na mayar da wasu sassan Babban Bankin zuwa Legas ne sai kuma ga wata sanarwa daga ma’aikatar Sufurin Jiragen sama inda ta sanar da aniyyarta ta mayar da wasu sassan Hukumar Kula da Filayen Jiaragen Sama (FANN) zuwa Legas. A cewarta, an yanke shawarar haka ce saboda rashin isassun ofishoshi a Abuja da kuma yawan aikin da ake fuskanta a bangaren hukumar na Legas.

Bayanin ya kuna nuna cewa, daga cikin manyan daraktoci 40 da hukumar ta nada a kwanan nan, 8 ne kawai suka fito daga arewacin Nijeriya, wanda hakan ke nuna alamun kamar akwai lauje cikin nadi.

CBN
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

MASU ALAKA

Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

June 8, 2026
Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

June 8, 2026
Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna
Manyan Labarai

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

June 8, 2026
Next Post
Yadda Arewa Ta Yi Shirin Yi Wa Matsalar Tsaro Taron Dangi

Yadda Arewa Ta Yi Shirin Yi Wa Matsalar Tsaro Taron Dangi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Ilimi Ne Babban Makamin Daƙile Ta’addanci — Ministan Tsaro

June 8, 2026
Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

June 8, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Gwamnatin Borno Ta Musanta Biyan Kuɗin Fansa Domin Kuɓutar da Mutane 360

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

June 8, 2026
Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

June 8, 2026
Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

June 8, 2026
Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

June 8, 2026
Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

June 8, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.