ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

by El-Zaharadeen Umar
1 month ago
Iyakoki

Kimanin shekaru goma ke nan wasu daga cikin iyakokin Nijeriya da Nijar ke garkame bisa umarnin gwamnatin tarayya wanda ta ce akwai dalilai na tsaro kamar yadda suka taba ambata wa.

To, sai dai rufe wadannan kan iyakoki na cigaba da zaizaye yanayi da karfin tattalin arzikin ‘yan kasa musamman wadanda suke huldar saye da sayarwa ta hanya sahihiya.

A lokuta daban-daban gwamnatin Nijeriya karkashin jagorancin marigayi Muhammad Buhari ta dage cewa ana amfani da kan iyakokin wajen shigowa da makamai da kuma haramtattun kwayoyi zuwa Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Hatta gidajen mai da suke da alaka da wasu garuruwan kan iyaka sun fuskanci irin wannan yanayi wanda har yanzu wasu gidajen mai a rufe suke sakamakon wancan mataki da gwamnatin tarayya ta dauka.

Sannu a hankali wannan matsala ta rufe kan iyakoki na cigaba da zama babbar barazana ga harkokin yau da kullum da kuma durkusar da tattalin arziki musamman al’ummomin da ke da alaka da iyakokin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

Farkon wannan gwamnati ta shugaba Tinubu ta bayyana aniyar ta na bude kan iyakoki amma daga baya, sai ta bude wasu ta bar sauran a rufe ba tare da karin haske ba.

Jihar Katsina tana da iyaka da kasar Nijar wanda a lokacin baya an yi hada hadar kasuwanci ta sahihiyar kuma amintacciyar hanya, a ya yin da wani bangare ake samun masu fasa kwabri wadanda ke bi ta barauniyar hanya.

Akwai iyakoki guda biyar da suke karkashin kulawar jami’an hukumar hana fasa kwabri ta kasa reshen jihar Katsina, amma babu wanda ke bude a hukumance a halin yanzu.

Wannan yanayi na cigaba da ta’azara musamman sabbin dokokin da kasar Nijar ke bijiruwa da su domin amfanin kasar su, wanda hakan ba karamin illa yake yi wa kasuwanci da ‘yan kasuwar Nijeriya ba

Bana shekaru biyu ke nan da gwamnatin Nijar ta hana shigowa da ragona zuwa Nijeriya ta wadannan kan iyakoki guda biyar da ke karkashin jihar Katsina wanda hakan ya taimaka wajen tsadar dabbobi a lokacin Sallah.

Mahukunta a kasar Nijar ba sa daukar abu da wasa, idan aka ce wannan abu doka ne, to, abinda zai raba ka da su lafiya shi ne, a kiyaye, idan kuma aka kuskure to hukunci sai ya tabbata.

Baya ga hana shigowa da dabbobi da gwamnatin Nijar ta yi, yanzu haka gwamnatin ta hana shigowa da man fetur zuwa Nijeriya domin yanzu man fetur din Nijar ya fi na Nijeriya sauki sakamakon fadan da ake gwabzawa tsakanin Amurka da Isra’ila da kuma Iran.

Kasar Nijar ta dai rage kudin man fetur din ta, maimakon karawa, saboda haka man fetur din Nijar ya fi na Nijeriya sauki, amma sun hana shigo shi zuwa Nijeriya bisa wasu dalilan da ba su bayyana ba a hukumance.

Wani abu da ke ciwa ‘yan kasuwa da masu haya da motoci akan iyakokin Nijeriya da Nijar tuwo  a kwarya yanzu shi ne, wata sabuwar doka da gwamnatin Nijar ta bullo da ita, ta hana direbobi daukar fasinjoji cikin mota fiye da mutum daya shiga kasar Nijar din kai tsaye.

Yanzu duk motar hanyar da zata shiga Nijar daga Nijeriya ba zata dauki fiye da mutum guda ba, sai dai idan ta shiga Nijar din ta dauki ko mutum nawa suke iya dauka.

Lamarin da ya kai inda ya kai, inda mafiyawancin ‘yan kasuwa ke kokawa akan wannan sabbin dokokin kasar Nijar da ta bijiru da su, bayan wadanda ake fama da su tuntuni.

A wani taron tattaunawa da hukumar hana fasa kwabri ta kasa ta shirya tsakanin ‘yan jaridu da jami’an ta a jihar Kano kakakin hukumar na kasa Abdullahi Aliyu Maiwada ya yi karin haske game da wannan aika-aika da ake zargin gwamnatin tarayya ta yi.

Taron dai an shirya shi ne bisa dalilin kara fahimtar juna da kulla alaka tsakanin ‘yan jaridu da jami’an hukumar kwastom domin samun nasarar da ake bukata.

Kakakin ya tabbatar da cewa har yanzu wadannan kan iyakoki suna rufe wanda ya ce ba zai iya bayyanawa al’umma dalili ba saboda yanayi na aiki da kuma tsaron kasa

Rufe kan iyakoki dai na cigaba da kawo bakin sauyi a yanayi da siga irin ta kasuwanci musamman al’ummomin da suke da alaka da kan iyakokin Nijeriya da Nijar.

Iyakoki
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina

MASU ALAKA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Rahotonni

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

July 25, 2026
Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe
Rahotonni

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

July 25, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci
Rahotonni

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Next Post
Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

July 25, 2026
Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

July 25, 2026
Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

July 25, 2026
Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

July 25, 2026
Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

July 25, 2026
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

July 25, 2026
Baya Ga “Sanyi Irin Na Sin”, Akwai Wasu Abubuwa Da Yawa Da Masu Yawon Bude Ido Na Turai Ke Sha’awa Kan Kasar

Baya Ga “Sanyi Irin Na Sin”, Akwai Wasu Abubuwa Da Yawa Da Masu Yawon Bude Ido Na Turai Ke Sha’awa Kan Kasar

July 25, 2026
Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

July 25, 2026
Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi Ya Yi Kira A Karfafa Hadin Gwiwa Na Kut-Da-Kut A SCO Domin Gina Duniya Mai Damawa Da Mabambantan Bangarori

Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi Ya Yi Kira A Karfafa Hadin Gwiwa Na Kut-Da-Kut A SCO Domin Gina Duniya Mai Damawa Da Mabambantan Bangarori

July 25, 2026
Kalolin Kitso Na Zamani: Yadda Ake Yin Fulani Style

Muhimmancin Kula Da Gashi Domin Lafiyarsa Da Kyawunsa

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.