ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

by El-Zaharadeen Umar
3 weeks ago
Iyakoki

Kimanin shekaru goma ke nan wasu daga cikin iyakokin Nijeriya da Nijar ke garkame bisa umarnin gwamnatin tarayya wanda ta ce akwai dalilai na tsaro kamar yadda suka taba ambata wa.

To, sai dai rufe wadannan kan iyakoki na cigaba da zaizaye yanayi da karfin tattalin arzikin ‘yan kasa musamman wadanda suke huldar saye da sayarwa ta hanya sahihiya.

A lokuta daban-daban gwamnatin Nijeriya karkashin jagorancin marigayi Muhammad Buhari ta dage cewa ana amfani da kan iyakokin wajen shigowa da makamai da kuma haramtattun kwayoyi zuwa Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Hatta gidajen mai da suke da alaka da wasu garuruwan kan iyaka sun fuskanci irin wannan yanayi wanda har yanzu wasu gidajen mai a rufe suke sakamakon wancan mataki da gwamnatin tarayya ta dauka.

Sannu a hankali wannan matsala ta rufe kan iyakoki na cigaba da zama babbar barazana ga harkokin yau da kullum da kuma durkusar da tattalin arziki musamman al’ummomin da ke da alaka da iyakokin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

Farkon wannan gwamnati ta shugaba Tinubu ta bayyana aniyar ta na bude kan iyakoki amma daga baya, sai ta bude wasu ta bar sauran a rufe ba tare da karin haske ba.

Jihar Katsina tana da iyaka da kasar Nijar wanda a lokacin baya an yi hada hadar kasuwanci ta sahihiyar kuma amintacciyar hanya, a ya yin da wani bangare ake samun masu fasa kwabri wadanda ke bi ta barauniyar hanya.

Akwai iyakoki guda biyar da suke karkashin kulawar jami’an hukumar hana fasa kwabri ta kasa reshen jihar Katsina, amma babu wanda ke bude a hukumance a halin yanzu.

Wannan yanayi na cigaba da ta’azara musamman sabbin dokokin da kasar Nijar ke bijiruwa da su domin amfanin kasar su, wanda hakan ba karamin illa yake yi wa kasuwanci da ‘yan kasuwar Nijeriya ba

Bana shekaru biyu ke nan da gwamnatin Nijar ta hana shigowa da ragona zuwa Nijeriya ta wadannan kan iyakoki guda biyar da ke karkashin jihar Katsina wanda hakan ya taimaka wajen tsadar dabbobi a lokacin Sallah.

Mahukunta a kasar Nijar ba sa daukar abu da wasa, idan aka ce wannan abu doka ne, to, abinda zai raba ka da su lafiya shi ne, a kiyaye, idan kuma aka kuskure to hukunci sai ya tabbata.

Baya ga hana shigowa da dabbobi da gwamnatin Nijar ta yi, yanzu haka gwamnatin ta hana shigowa da man fetur zuwa Nijeriya domin yanzu man fetur din Nijar ya fi na Nijeriya sauki sakamakon fadan da ake gwabzawa tsakanin Amurka da Isra’ila da kuma Iran.

Kasar Nijar ta dai rage kudin man fetur din ta, maimakon karawa, saboda haka man fetur din Nijar ya fi na Nijeriya sauki, amma sun hana shigo shi zuwa Nijeriya bisa wasu dalilan da ba su bayyana ba a hukumance.

Wani abu da ke ciwa ‘yan kasuwa da masu haya da motoci akan iyakokin Nijeriya da Nijar tuwo  a kwarya yanzu shi ne, wata sabuwar doka da gwamnatin Nijar ta bullo da ita, ta hana direbobi daukar fasinjoji cikin mota fiye da mutum daya shiga kasar Nijar din kai tsaye.

Yanzu duk motar hanyar da zata shiga Nijar daga Nijeriya ba zata dauki fiye da mutum guda ba, sai dai idan ta shiga Nijar din ta dauki ko mutum nawa suke iya dauka.

Lamarin da ya kai inda ya kai, inda mafiyawancin ‘yan kasuwa ke kokawa akan wannan sabbin dokokin kasar Nijar da ta bijiru da su, bayan wadanda ake fama da su tuntuni.

A wani taron tattaunawa da hukumar hana fasa kwabri ta kasa ta shirya tsakanin ‘yan jaridu da jami’an ta a jihar Kano kakakin hukumar na kasa Abdullahi Aliyu Maiwada ya yi karin haske game da wannan aika-aika da ake zargin gwamnatin tarayya ta yi.

Taron dai an shirya shi ne bisa dalilin kara fahimtar juna da kulla alaka tsakanin ‘yan jaridu da jami’an hukumar kwastom domin samun nasarar da ake bukata.

Kakakin ya tabbatar da cewa har yanzu wadannan kan iyakoki suna rufe wanda ya ce ba zai iya bayyanawa al’umma dalili ba saboda yanayi na aiki da kuma tsaron kasa

Rufe kan iyakoki dai na cigaba da kawo bakin sauyi a yanayi da siga irin ta kasuwanci musamman al’ummomin da suke da alaka da kan iyakokin Nijeriya da Nijar.

Iyakoki
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai
Rahotonni

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Noma
Rahotonni

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Next Post
Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

LABARAI MASU NASABA

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.