ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Fuskanci Kalubale Daga Mutanen Da Har Yanzu Ba Su Fahimci Fim Ba –Ibrahim Gungu

by Rabi'at Sidi Bala
4 years ago
Fim

A wannan makon mun kawo muku karashen tattaunawa da Ibrahim Gungu wanda aka fi sani da “Bawan Mata”. Inda a wannan karon ya bayyana wakokin da ya yi da kuma abin da ya shafi kalubale na sana’ar fim, kamar yadda suka tattauna da wakiliyarmu RABI’AT SIDI.

Mu koma ga batun waka, kafin ka bar waka ka yi wakokin sun kai kamar guda nawa, kuma a cikin wakokin ko akwai wadda ta zaga aka santa a gari?
Na yi wakoki da yawa, adadinsu zai kai 100, to amma wasu ma ba ni na rera su da muryata ba, akwai wadanda suka zagaya sosai kamar su, SO DA HAWAYE, wakar ta zagaya sosai kuma ta samu karbuwa. To amma ita Sunusi Anu shi ne ya rera ta, bayan an yi min kida a ‘studio’ na rera da muryata sai aka cire tawa shi ya dora tasa.

  • Fim Sana’a Ce Mai Alfarma Da Albarka – Ibrahim Gungu

Tun bayan da ka bar harkar waka shin baka ji kana sha’awar komawa yi ba, ko kuwa yanzu ka fi son ka tsaya iya abin da ya shafi fim kawai?
Gaskiya ba na sha’awar komawa, na fi son in tsaya a bangaren fim kawai.

ADVERTISEMENT
Fim
Ibrahim Gungu

Ko akwai wani kalubale da ka taba fuskanta game da fim?
To kalubale akan rayuwar dan’Adam ai ba a rasawa. Na fuskanci kalubale a kan wasu mutane wadanda har yanzu su basu fahimci meye fim ba, kuma ba su fahimci abin da fim ke nufi ba.

To ya batun nasarori fa, wadanne irin nasarori ka samu game da fim?
Alhamdulillah ma sha Allah, dukkakan wata nasara da mutum yake samu a dalilin fim Allah ya bani ita. Misali; nasara ta farko masoya, ka yi abu mutane su ce suna so kuma su rika bibiya suna yabawa kuma suna godewa, shima arziki ne, nasara ce, sannan na samu arziki da alkairi da kyaututtuka kala-kala a dalilin fim to kin ga sai dai in ce Alhamdulillah.

LABARAI MASU NASABA

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

Ya ka dauki fim a wajenka?
Wani babban al’amari, saboda ni fim a wajena sana’a ce kuma hanya ce da nake isar da sakona ga al’umma iri daban-daban.

Wane buri kake son cimma game da fim?
To burina akan fim yana da yawa, kadan daga ciki, (1) in rika kai sakona na fadakarwa da ilimantarwa ga al’umma, (2) Allah ya kara min dauka ka a fadin duniya ya zama inda ma ba a sanni ba a sanni, (3) masu mugwayen hali in rika kakkawo karshensu domin ya zama izna ga mutane.

Fim
Ibrahim Gungu

Wane ne babban abokinka a cikin masana’antar Kannywood?
Abokaina suna da yawa, amma dai wanda a ko da yaushe muna tare da shi shi ne Isah Bawa Doro.

Da wa ka fi so a hadaka a fim?
Gaskiya ne ba ni da zabi akan abokan aiki. Kowa aka hada ni da shi matukar shi ma ya fahimci aiki, to za mu yi tare kuma ‘Director’ zai samu abin da yake so.

Wa ya fi birgeka a cikin sauran jarumai?
Ni ai kowa nawa ne, duk wanda ya yi abin kirki akan aikin zai birge ni kuma zan jinjina masa.

Wanne abu ne ya taba faruwa da kai a rayuwa na farin ciki ko akasin haka, wanda ba za ka taba iya mantawa da shi ba?
Akwai na farin ciki sun fi adadin lissafi, wata rana ba na tunani ba na tsammani kawai sai wani masoyina ya kira ni a waya ya ce ga kyautar mota nan ya turo a kawo min, da fada min da yai da zuwan motar bai wuce awa biyu ba. Gaskiya na ji dadin wannan kyautar kuma ba zan taba mantawa da ita ba tun da a lokacin ma motar da ya bani, ba ni da ikon sayenta. Abin da ya taba faruwa da ni na rashin dadi a rayuwa ta wanda bana mantawa da shi shi ne rasuwar mahaifiyata, ta tashi lafiya kalau ba ciwo da Asuba ranar juma’a ta je bandaki ta dawo ta yi alwala a nan take Allah ya karbi ranta.

Mene ne burinka na gaba game da fim?
In sha Allah zan ci gaba da kokari ba ranar dainawa, sannan kuma in ci gaba da yin fadakarwa akan addini da kuma yadda rayuwa ya kama ta tafi.

To ya batun iyali shin akwai ko kuma tukunna dai?
Ina da mata da ‘ya’ya guda 3

To ya batun kari, shin za ka kara ko kuwa ba ka da ra’ayin hakan?
Wannan ai na Allah ne, idan na samu mai natsuwa mai hankali da ilimi da tarbiyya, kuma mai so na tsakani da Allah in sha Allah zan kara.

Misali wata a cikin abokan aikinka ta ce tana sonka za ta aureka shin za ka amince da hakan ko kuwa ba ka da ra’ayin aurar abokiyar aiki?
Kwarai kuwa, ina da ra’ayi idan Allah ya hada hankalinmu da ita ba wani matsala zan aureta.

Wacce shawara za ka bawa masu kokarin shiga harkar fim?
To Alhamdulillahi shawarar da zan basu ita ce duk mai sha’awar shiga fim to ya sani ita sana’a ce ta hukuri sai an yi hakuri ci gaba yake zuwa ba lokaci daya ba.

Ko akwai wani kira da za ka yi ga abokan sana’arka ta fim?
Ina kira ga abokan sana’a ta da mu kara jin tsoron Allah kuma ko mai mutum zai yi ya sani Allah zai tambaye shi. Mu ci gaba da aika wa al’umma sako na addini da nasiha da kuma fadakarwa a cikin ayyukan mu da muke yi na fina-finanmu.

Ko akwai wani kira da za ka yi ga gwamnati game da sana’arku ta fim?
Gwamnati ta kalli masana’artar Kannywood da idon albarka, ba kallon hadarin kaji ba. Su fahimci cewa mu fa taimakon su muke yi, saboda da yawa akwai wadanda suka gama makarantun Boko, ba su samu aikin yi ba a gwamnatance, amma sun samu aiki a masana’artar Kannywood, wanda hakan ya ragewa matasa zaman kashe wando a kasar nan. Amma da yawa za ki ji ana wasu abubuwa da suka shafi tallafa wa masana’antu a kasar nan, amma mu sai dai mu ji a salansa. Wani lokacin kuma sai dai mu ji takwarorinmu na Kudancin kasar nan (Nollywood) sun amfana mu an mai da mu saniyar ware. Don haka ina kara kira ga gwamnati da ta kara jawo ‘yan Kannywood a jikinta.

Me za ka ce da masoyanka?
To masoyana maza da mata ina godiya sosai Allah ya bar mu tare da ku Allah ya bar zumunci, kuma Allah ya kara daukaka mu ni da ku baki daya. Allah ya bamu lafiya da zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar mu baki daya Allah ya zaba mana shuwagabanni nagari.

Me za ka ce da ita kanta Jaridar Leadership Hausa?
Jaridar LEADERSHIP ja gayya ce a cikin kafofin yada labarai na Nijeriya. Bugu da kari LEADERSHIP wata kafa ce da ta kware wurin bincike na musamman tare da fitar da mutane duhu akan al’amurran da suke faruwa a kasar nan. Akwai mutane da dama wadanda suke zaune a cikin gida ko ‘office’ ba su zuwa ko ina, amma bibiyar LEADERSHIP ya sa duniya ta zamo a tafin hannunsu. Saboda kwarewarsu aiki mun gani, sun samu mabambantan karramawa, babu ruwansu, da akida ko bangarenci, gaskiya wannan gidan jaridar abun a yaba ne. Haka zalika ga dama da suke ba irin mu domin tofa albarkacin bakinsu, akan harkokinmu na yau da kullum.
Babu abin da za mu ce, sai dai Allah ya kara daukaka. Sannan Muna kira ga masoyanmu da su ci gaba da bibiyar LEADERSHIP Hausa musamman wannan shafi na Rumbun Nishadi, domin jin labaran da suka shafi fadakarwa, ilimantarwa, har ma da nishadantarwa, na gode.

Ko kana da wadanda za ka gaisar?
Ina gaishe da daukacin ma’aikatan wannan gidan jaridar ta bangaren Hausa da Turanci, da kuma ke kanki, da ki ke kokarin gabatar da wannan shiri. Sannan godiya ga babban ‘Director’ Ibrahim Bala.

Muna godiya
To Alhamdulillah ni ma ina godiya Allah ya bamu nasara.

Fim
Rabi'at Sidi Bala
+ postsBio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Dalilan Da Suka Jawo Aka Ƙi Yin Maraba Da FIM House A Jihar Kano
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Next Post
Li Keqiang Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Dandalin Tattaunawa A Fannin Kirkire-kirkire Na Pujiang Na Shekarar 2022

Li Keqiang Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Dandalin Tattaunawa A Fannin Kirkire-kirkire Na Pujiang Na Shekarar 2022

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.