Sakatare janar na kwamitin kolin JKS Xi Jinping, ya jagoranci wani taro na ofishin kula da harkokin siyasa na kwamitin kolin, domin nazarta da tsara ayyukan da suka shafi takaita illolin ambaliya da rage radadin fari.
A cewar taron, ana sa ran samun karin tsanantar yanayi irin wanda ba a saba gani ba a bana, a lokacin da aka fi samun ambaliya a kasar Sin, inda za a samu fari da ambaliya a lokaci guda.
Taron ya bukaci dukkan yankuna da sassa masu ruwa da tsaki, su dauki matakai masu kwari na tabbatar da an takaita illolin ambaliya da rage radadin fari da kai daukin gaggawa da rigakafin aukuwar ibtila’i.
Da yake nanata kare rayukan jama’a a matsayin abu mafi muhimmanci, taron ya yi kira da a dauki matakan karfafa takaita ambaliya a kan manyan koguna da tabkuna tare da bayyana bukatar bayar da muhimmancin gaske ga barazanar ganin sauyin kwatsam tsakanin ambaliya da fari da kuma karfafa daukar matakan bai daya na kulawa da rarraba ruwa.
Ya kuma nanata bukatar tabbatar da kare manyan kayayyakin more rayuwa da ayyukan gini da ake gudanarwa yayin lokacin na ambaliya da kuma daukaka kare kayayyakin aikin gona. (Fa’iza Mustapha)














