Jam’iyyar NDC ta bayyana cewa za ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ke Lokoja, wanda ya soke hukuncin da ya umarci Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta yi mata rajista.
Sakataren Yaɗa Labarai na jam’iyyar, Osa Director, ya ce za su fara nazarin hukuncin kotun kafin su ɗauki matakin ɗaukaka ƙara.
Mai shari’a Isah Dashen ya soke hukuncin da aka yanke a watan Disamban 2025 bayan jam’iyyar PMP ta ce ba a saka ta cikin shari’ar ba duk da cewa tana da ruwa da tsaki a lamarin.
Kotun ta umarci a sake sauraron shari’ar tare da haɗa dukkanin ɓangarorin da abin ya shafa.
PMP ta yi zargin cewa NDC ta yi amfani da tambarin da ita ta taɓa mika wa INEC.
Duk da hukuncin, NDC ta ce tana mutunta kotun, amma za ta ci gaba da neman haƙƙinta ta hanyar ɗaukaka ƙara, tana mai nuna ƙwarin gwiwar cewa kotun gaba za ta yi mata adalci.














