A madadin kasashe kusan 20 kasar Sin ta gabatar da sanarwar hadin gwiwa a jiya Alhamis, yayin zaman majalisar kare hakkin dan Adam ta MDD wadda ke taronta karo na 62, inda cikin sanarwar aka fallasa, tare da yin Allah wadai da matakan danniya na daukar matsayar kashin kai ta hanyar kakabawa wasu sassa haraji ba gaira ba dalili, ta fakewa da wai “Ana tilasawa jama’a yin kwadago ala tilas”.
Jakadan kasar Sin a ofishin MDD dake Geneva, da sauran kungiyoyin kasa da kasa dake Switzerland Jia Guide ne ya gabatar da sanarwar hadin gwiwar. Sanarwar ta ce, kawar da talauci ya dogara ga damar baiwa dukkanin jama’a ikon yin aiki da samun ci gaba. Ta ce, “Muna matukar adawa da tilasta yin kwadago. Amma a lokaci guda, muna bayyana damuwa, da nuna matukar adawa da matakin kakaba karin harajin fito kan wasu kasashe, saboda kawai an zarge su da gaza dakile fitar da hajoji da aka samar ta hanyar wai “Kwadago na dole”.
Irin wadannan matakai a cewar sanarwar, ba abun da za su haifar, illa gurgunta tsarin duniya na samar da hajoji, da karya nasarar kokarin bai daya na sassan kasa da kasa dangane da kawar da talauci.
Kazalika, sanarwar ta hadin gwiwar ta jaddada kiran kasar Sin ga sauran kasashen duniya na martaba gaskiya, da kauracewa siyasantar da batutuwan cinikayya, da amfani da batun kare hakkin bil’adama a matsayin makamin tursasa wasu bangarori, kana su mara baya ga odar duniya ta raya tattalin arziki da cinikayya, da bayar da gudunmawar bunkasa ci gaban duniya ta hanyar aiwatar da matakai na hakika. (Saminu Alhassan)














