ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NED – Hannun Tsoma Baki Da Ke Sanye Da “Tufar Dimokuradiyya”

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 months ago
NED

Wani sabon rahoto na shekara-shekara da wata kungiya mai zaman kanta ta Amurka mai suna “National Endowment for Democracy” (NED) ta fitar, ya nuna wani salo da aka sani, kuma wanda ke kara tsananta, wato kungiyar na ci gaba da fadada samar da kudade ga cibiyoyinta domin ayyukan da suka shafi kasar Sin.

Cibiyoyin suna yin aikin tsoma baki cikin harkokin cikin gidan Sin da sunan “inganta dimokuradiyya”. Idan aka cire wannan “tufar dimokuradiyya”, za a iya ganin mugunyar fuskar NED a fili.

Na farko, asalin NED yana da fuska biyu: ta kira kanta kungiya mai zaman kanta, amma kudadenta kusan duka daga majalisar dokokin Amurka suke fitowa.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda daya daga cikin wadanda suka kafa kungiyar Allen Weinstein ya fayyace cewa, yawancin ayyukan da NED ke yi a yau, ayyuka ne da hukumar leken asiri ta CIA take yi a baya a boye.

Amma a yanzu ana gudanar da su a fili. Wannan kuma shi ne bambanci kadai, amma ainihin kudurin bai canza ba. Wannan shi ne dalilin da ya sa ake kiran NED a matsayin “Kura da fatar Akuya” ga Washington.Na biyu, NED tana ikirarin cewa tana “bai wa masu gudanar da gwagwarmaya da juyin mulki karfi”, to amma abun tambaya shi ne wadanne kungiyoyi ko mutane ne take karfafawa?A yankin Hong Kong na kasar Sin, an fallasa cewa NED tana tallafa wa kungiyoyin da suka tunzura yin zanga-zanga a lokacin tashin hankalin shekara ta 2019.

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

A jihar Xinjiang ta Sin, kungiyoyin da ta tallafawa sun dade suna jagorantar masu neman a sanyawa kasar Sin takunkumai. A Tibet, cibiyoyin yanar gizo da take tallafawa sun ci gaba da yada labaran karya. Wannan ba “inganta dimokuradiyya” ba ne, maimakon haka tallafawa wanzuwar dakaru masu adawa da Sin ne.Bari mu kuma dubi jerin tallafin da NED ta bayyana a fili – kungiyoyin adawa a Serbia, da na Georgia, da na Ukraine, da kasashen Gabas ta Tsakiya, wadanda daga karshe suka haifar da tarzoma da zubar da jini.

Daga gabashin Turai zuwa Gabas ta Tsakiya, irin wannan tsarin tallafi yana tare da rikice-rikicen siyasa na “juyin juya halin don hambarar da mulki”.

Yanzu, an aiwatar da irin wannan mataki a Sin, don horar da cibiyoyin kawo baraka a cikin gidan kasar Sin, tare da yaudarar tunanin sassan kasa da kasa kan abin da take aiwatarwa.

NED ba ’yar kallo ba ce. Tana shiga cikin aikin kawo wa Sin barazana da cin zarafinta. Kazalika, kudadenta na karuwa, hannunta na kara shiga dukkanin sassa, kuma manufarta ba za ta taba canzawa ba, wato tsoma baki bisa hujjar “dimokuradiyya”, shi ne ainihin fuskar NED. (Mai zane da rubutu: MINA)

NED
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya
NED
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

MASU ALAKA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
Daga Birnin Sin

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
Next Post
Xi: Ya Kamata a Yi Amfani Da “Kwarewar Ci Gaban Yiwu” Yadda Ya Kamata

Xi: Ya Kamata a Yi Amfani Da "Kwarewar Ci Gaban Yiwu" Yadda Ya Kamata

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.