ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NiMet Ta Yi Hasashen Ruwan Sama Da Wuri, Ta Nemi Manoma Su Jinkirta Shuka

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
4 months ago
Nimet

Hukumar Yanayi ta Nijeriya (NiMet) ta yi hasashen ruwan sama na farkon lokaci a Kano, Neja, Ribas da wasu jihohi goma sha biyu na tarayya.

Ministan Sufuri da Ci gaban Jiragen Sama, Festus Keyamo, SAN, ne ya bayyana haka a Abuja ranar Talata, yayin da ya kaddamar da Hasashen Yanayi na Lokutan Damina na 2026 (SCP) da NiMet ta shirya, inda ya gargadi manoma da su yi hattara kada su fara shuka iri kafin lokacin damina ya fara.

  • Sojoji Sun Ceto Mutane Takwas Da Aka Sace A Yayin Wani Bikin Aure A Shanono
  • Tsaro: Har Yanzu ‘Yan Ta’adda Na Ci Gaba Da Yi Wa Mutane Kisan Kiyashi A Arewa

Ministan ya ce, ko da yake an samu ruwan sama na farkon lokaci a wasu sassan kasar, kamar Lagos, Ribers, da Bayelsa da wasu, ainihin lokacin damina bai fara ba, inda ya jaddada cewa ana sa ran yanayi mai tsanani tsakanin Maris zuwa Mayu na wannan shekara.

ADVERTISEMENT

Hasashen SCP ya nuna yiwuwar samun ruwan sama mai yawa a yankunan kudu na kasar a wannan shekara, tare da hasashen farkon damina, karshen damina da yanayi mai tsanani a 2026.

Rahoton ya nuna cewa, ana sa ran farkon damina a Bayelsa, Ribers, Akwa Ibom, Cross Riber, Benue, Kogi, Nasarawa, Oyo, da wasu sassan Kebbi, Neja, Jigawa, Katsina, Kano, Adamawa, da Taraba. Yayin da a Borno ake sa ran fara damina ne a jinkiri.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Bugu da kari, rahoton ya nuna cewa karshen damina na iya kasancewa da wuri fiye da yadda aka saba a wasu sassan Ogun, Osun, Ondo, Imo, Ribers, Akwa Ibom, Kogi, da Neja. Sai dai kuma, a Lagos, Ogun, Anambra, Enugu, Cross Riber, Benue, Nasarawa, da Kaduna ana sa ran karshen damina zai jinkirta fiye da yadda aka saba.

Duk da haka, ana sa ran kakar ruwan sama zai kasance mai tsawo fiye da yadda aka saba a jihohi kamar Lagos, Benue, Enugu, Ebonyi, Ogun, Oyo, Nasarawa, Anambra, Kwara, Kebbi, Kaduna, Gombe da Taraba. Yayin da wasu sassan Borno, Yobe da Neja ake sa ran kakar ruwan sama zai kasance gajere fiye da yadda aka saba.

Ana sa ran adadin ruwan sama na shekara-shekara zai kasance daidai da yadda aka saba a mafi yawan sassan Nijeriya, idan aka kwatanta da matsakaicin tsawon lokaci. Ruwan sama fiye da kima ana sa ran a jihohi kamar Borno, Sokoto, Kebbi, Kaduna, Enugu, Cross Riber, Abia, Ebonyi, Akwa Ibom, da Babban Birnin Tarayya (FCT); yayin da a wasu sassan Katsina, Zamfara, Kwara, Oyo, da Ogun ake sa ran ruwan sama kasa da kima.

A lokacin kakar Maris zuwa Mayu, ana sa ran zafi da bushewa mai tsanani fiye da kwanaki 15 a wasu sassan Oyo da Ogun, yayin da bushewa mai matsakaici ake sa ran a jihohi kamar Ekiti, Kogi, Osun, Ondo, Ogun, Edo, Ebonyi, Abia, Cross Riber da Delta, da kuma wasu sassan Kogi da Kwara.

Bugu da kari, a lokacin kakar Yuni-July-Agusta, ana hasashen bushewa mai tsanani wanda zai iya kai wa kwanaki 21 a wasu sassan Bauchi, Borno, Gombe, Jigawa, Katsina, Kano, Kebbi, Kwara, Nasarawa, Neja, Oyo, Filato, Sokoto, Yobe, da Zamfara.

A gefe guda, ana hasashen samun karancin ruwa, wanda ake kira “August Break,” zai fara daga karshen watan Yuli, kuma zai kasance mai tsanani da tsawo a jihohi kamar Lagos, Ogun, Ekiti, da wasu sassa na Oyo. Adadin kwanakin da ba za a samu ruwan sama ba ko kadan zai kasance tsakanin kwanaki 28 zuwa 40. Ana sa ran tasirin matsakaicin karancin ruwan sama a jihohi kamar Ondo, da wasu sassan Kwara da Edo.

Babban Sakataren Ma’aikatar Jiragen Sama da Ci gaban Sararin Samaniya, Dr. Yakubu Adam Farmata, ya bayyana cewa SCP na ci gaba da zama wata muhimmiyar hanya ta karfafa hadin gwiwa tsakanin kimiyyar yanayi da tsara ci gaban kasa.

Ya ce gabatar da Hasashen Yanayi na Shekara ba kawai aikin kimiyya ba ne, amma wata muhimmiyar tattaunawar kasa ce da ke nufin karfafa shiri da aiwatar da tsare-tsaren ci gaban kasa.

Nimet
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
Nimet
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Nimet

Har Yanzu Dai Kan Batun Tu’ammali Da Kayan Maye A Nijeriya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.