Hukumar Yanayi ta Nijeriya (NiMet) ta yi hasashen ruwan sama na farkon lokaci a Kano, Neja, Ribas da wasu jihohi goma sha biyu na tarayya.
Ministan Sufuri da Ci gaban Jiragen Sama, Festus Keyamo, SAN, ne ya bayyana haka a Abuja ranar Talata, yayin da ya kaddamar da Hasashen Yanayi na Lokutan Damina na 2026 (SCP) da NiMet ta shirya, inda ya gargadi manoma da su yi hattara kada su fara shuka iri kafin lokacin damina ya fara.
- Sojoji Sun Ceto Mutane Takwas Da Aka Sace A Yayin Wani Bikin Aure A Shanono
- Tsaro: Har Yanzu ‘Yan Ta’adda Na Ci Gaba Da Yi Wa Mutane Kisan Kiyashi A Arewa
Ministan ya ce, ko da yake an samu ruwan sama na farkon lokaci a wasu sassan kasar, kamar Lagos, Ribers, da Bayelsa da wasu, ainihin lokacin damina bai fara ba, inda ya jaddada cewa ana sa ran yanayi mai tsanani tsakanin Maris zuwa Mayu na wannan shekara.
Hasashen SCP ya nuna yiwuwar samun ruwan sama mai yawa a yankunan kudu na kasar a wannan shekara, tare da hasashen farkon damina, karshen damina da yanayi mai tsanani a 2026.
Rahoton ya nuna cewa, ana sa ran farkon damina a Bayelsa, Ribers, Akwa Ibom, Cross Riber, Benue, Kogi, Nasarawa, Oyo, da wasu sassan Kebbi, Neja, Jigawa, Katsina, Kano, Adamawa, da Taraba. Yayin da a Borno ake sa ran fara damina ne a jinkiri.
Bugu da kari, rahoton ya nuna cewa karshen damina na iya kasancewa da wuri fiye da yadda aka saba a wasu sassan Ogun, Osun, Ondo, Imo, Ribers, Akwa Ibom, Kogi, da Neja. Sai dai kuma, a Lagos, Ogun, Anambra, Enugu, Cross Riber, Benue, Nasarawa, da Kaduna ana sa ran karshen damina zai jinkirta fiye da yadda aka saba.
Duk da haka, ana sa ran kakar ruwan sama zai kasance mai tsawo fiye da yadda aka saba a jihohi kamar Lagos, Benue, Enugu, Ebonyi, Ogun, Oyo, Nasarawa, Anambra, Kwara, Kebbi, Kaduna, Gombe da Taraba. Yayin da wasu sassan Borno, Yobe da Neja ake sa ran kakar ruwan sama zai kasance gajere fiye da yadda aka saba.
Ana sa ran adadin ruwan sama na shekara-shekara zai kasance daidai da yadda aka saba a mafi yawan sassan Nijeriya, idan aka kwatanta da matsakaicin tsawon lokaci. Ruwan sama fiye da kima ana sa ran a jihohi kamar Borno, Sokoto, Kebbi, Kaduna, Enugu, Cross Riber, Abia, Ebonyi, Akwa Ibom, da Babban Birnin Tarayya (FCT); yayin da a wasu sassan Katsina, Zamfara, Kwara, Oyo, da Ogun ake sa ran ruwan sama kasa da kima.
A lokacin kakar Maris zuwa Mayu, ana sa ran zafi da bushewa mai tsanani fiye da kwanaki 15 a wasu sassan Oyo da Ogun, yayin da bushewa mai matsakaici ake sa ran a jihohi kamar Ekiti, Kogi, Osun, Ondo, Ogun, Edo, Ebonyi, Abia, Cross Riber da Delta, da kuma wasu sassan Kogi da Kwara.
Bugu da kari, a lokacin kakar Yuni-July-Agusta, ana hasashen bushewa mai tsanani wanda zai iya kai wa kwanaki 21 a wasu sassan Bauchi, Borno, Gombe, Jigawa, Katsina, Kano, Kebbi, Kwara, Nasarawa, Neja, Oyo, Filato, Sokoto, Yobe, da Zamfara.
A gefe guda, ana hasashen samun karancin ruwa, wanda ake kira “August Break,” zai fara daga karshen watan Yuli, kuma zai kasance mai tsanani da tsawo a jihohi kamar Lagos, Ogun, Ekiti, da wasu sassa na Oyo. Adadin kwanakin da ba za a samu ruwan sama ba ko kadan zai kasance tsakanin kwanaki 28 zuwa 40. Ana sa ran tasirin matsakaicin karancin ruwan sama a jihohi kamar Ondo, da wasu sassan Kwara da Edo.
Babban Sakataren Ma’aikatar Jiragen Sama da Ci gaban Sararin Samaniya, Dr. Yakubu Adam Farmata, ya bayyana cewa SCP na ci gaba da zama wata muhimmiyar hanya ta karfafa hadin gwiwa tsakanin kimiyyar yanayi da tsara ci gaban kasa.
Ya ce gabatar da Hasashen Yanayi na Shekara ba kawai aikin kimiyya ba ne, amma wata muhimmiyar tattaunawar kasa ce da ke nufin karfafa shiri da aiwatar da tsare-tsaren ci gaban kasa.















Discussion about this post