ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Dai Kan Batun Tu’ammali Da Kayan Maye A Nijeriya

by Leadership Hausa and Sulaiman
4 months ago
Maye

Hukumar da ke yaki da safara da tu’ammali da kayan maye wato NDLEA, a kwanan baya, ta sanar da cewa, ‘yan Nijeriya da shekarun su, suka fara daga tsakanin 15, zuwa 64, su sama da miliyan 15, an tabbatar suna shan kayan mayen.

Da yake buga misali da, wani bincike da Majalisar Dinkin Duniya ta gudanar a 2018, Shugaban NDLEA na kasa Birgediya Janar Mohammed Buba Marwa mai murabus, ya bayyana cewa, duk mutum daya, a cikin mutane bakwai na ‘yan kasar da ke a tsakanin wadannan shekarun, na yin wannan mummunar dabi’ar, inda alkaluman suka nuna cewa, yawan ya kai rubi uku, na masu tu’ammalin a kasar, a fadin duniya.

  • Zargin Da Amurka Ta Yi Wa Sin Game Da Gwajin Nukiliya Ba Shi Da Tushe
  • Mu’amala Tsakanin Shugabannin Sin Da Amurka Tana Taka Muhimmiyar Rawa A Dangantakar Kasashen

Kazalika, wasu alkaluma da hukumar ta fitar a hukumance, sun nuna cewa, daga tsakanin 2021 zuwa 2026 NDLEA, a daukacin fadin kasar, ta yi kamen da ke da alaka da shan kayan mayen, da suka kai adadin dubu 77,792.

ADVERTISEMENT

Kamen ya hada da na dai-daikun shaharattun masu sayar da kayan maye   guda 28 da kuma wasu manyan jiga-jigan dilolin kayan maye, da suka shahara a duniya.

Bugu da kari, a dai tsakanin wadannan shekarun, NDLEA ta samu nasarar a gaban Kotu, na ganin an gurfanar tare da kuma yankewa wadanda aka kama da laifikasar, 14,225 hukunci, a gaban kotu.

LABARAI MASU NASABA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

Ta alakanta wannan sanarar ga babbar karfafa hadaka da ta samu daga bangaren Shari’ar kasar.

Wannan Jaridar, ta damu matuka,  kan kara samun lamuran da suka shafi, yin tu’ammali da kayan mayen a kasar, musamman ganin yadda dabi’ar ta zama tamkar ruwan dare, a tsakanin wasu matasan kasar duk da kokarin da NDLEA ke ci gaba da yi, na yakar dabi’ar.

Matasa dai, sune kashin bayan kowacce irin alumma, amma abin bakin ciki, su ne, kan gaba wajen yin dabi’ar inda hakan ke janyo wasu su haukace ko kuma shaye-sahyen, ya shafi lafiyarsu.

Bisa wani bincike da aka gudanar, ya nuna cewa, shiyyar Kudu Maso Gabas, musamman a jihohin Legas, Oyo, Ogun, da Ondo, nan ne ke kan gaba a yin dabi’ar, inda suke da kaso 24 a cikin dari, sai kuma Kudu Maso Kudu da ke da kaso 18.

Bugu da kari, a Arewa Maso Yanna kuwa, akasari an fi tu’ammali da codeine syrup, inda kuma a Arewa Maso Gabas, musamman a jihohin Gombe, Yobe, Adamawa, da Bauchi, nan ma lamarin, yayi kamari.

Butun na shan kayan mayen, abu ne, dai da zama tamkar gobarar Jeji, a fadin duniya, duba da alkaluman da ofishin majalisar dinkin duniya da ke yaki da shan kaya maye, ya fitar, inda alkaluman suka nuna cewa, akalla masu tu’ammali da kayan maye a 2020, sun kai miliyan 284.

Kazalika, a cikin wani rahoto da majalisar dinkin duniya ta fitar a 2022, ya ce, ana noman Tabar Wiwi, a kasashe 154 tare da kuma kayan maye na opium, da ake nomawa a kasashe  57.

Hakazalika, NDLEA ta sanar da cewa, daga cikin tan dubu 15,000 na nau’ukan kayan maye da ta kwace, a shekaru biyar da suka wuce, sama da kaso 75, duk na Tabawar Wiwi ne.

Wannan Jaridar na da yakin cewa, musamman bisa dogaro kan wani bincike da aka gudanar, ya nuna cewa, shan kayan maye, musamman cocaine, na bai wa masu sha, aikata manyan laifuka.

Misali, irin ayyukan rashin imani da ‘yan ta’addar kungiyar Boko Haram da masu garkuwa da mutane ke aikatawa, suna da nasaba sham muggan kayan maye.

Akwai dai, matukar bukatar mahukunta a kasar nan, su kara daura damarar kawo karshen wannan mummunar dabi’ar.

Idan za a iya tunawa, a 2024 musamman kan aikin da majalisar dattawa ke yi, na yiwa kundin tsarin mulkin kasar garanbawul, ta bayar da shawara da a samar da wata doka da za ta bayar da damar, yanke hukunci, ga masu safarar miyagun kwayoyi, musamman hukuncin, ya kasance na kisa.

Idan kuma ba  hukuncin kisa ba, a yiwa masu safarar tsatsaruan hukunci na  zaman gidan kaso daga shekaru 15 25, ba tare da cin wata tara ba.

Wani karin abin takaicin, a duk kokacin da ake gudanar da zagayowar ranar yaki da shan kayan maye ta duniya, za a ga, mawaka da dauko domin gangamin wayar kai kan yakin, suma a wajen taron, suna ta faman shan kayan mayen a bainar jama’a, inda su kuma jami’an tsaro, basa taka masu birki.

Karin wani abin bakin cikin shi ne, yadda ake yin amfani da Tashohin Jiragen Ruwan kasar, wajen yin safarar muggan kayan maye.

A ra’ayinmu, muna ganin akwai matukar bukatar a samar da kyawawan dabaru da limantar wa alumma, kuma hukumomin kasar su kara jajircewa, wajen yakar dabi’ar a kasar.

Maye
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Maye
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

May 15, 2026
Next Post
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Manoma Da Makiyaya Sun Kulla Yarjejeniyar Zaman Lafiya A Filato

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.