ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Dai Kan Batun Tu’ammali Da Kayan Maye A Nijeriya

by Leadership Hausa and Sulaiman
4 months ago
Maye

Hukumar da ke yaki da safara da tu’ammali da kayan maye wato NDLEA, a kwanan baya, ta sanar da cewa, ‘yan Nijeriya da shekarun su, suka fara daga tsakanin 15, zuwa 64, su sama da miliyan 15, an tabbatar suna shan kayan mayen.

Da yake buga misali da, wani bincike da Majalisar Dinkin Duniya ta gudanar a 2018, Shugaban NDLEA na kasa Birgediya Janar Mohammed Buba Marwa mai murabus, ya bayyana cewa, duk mutum daya, a cikin mutane bakwai na ‘yan kasar da ke a tsakanin wadannan shekarun, na yin wannan mummunar dabi’ar, inda alkaluman suka nuna cewa, yawan ya kai rubi uku, na masu tu’ammalin a kasar, a fadin duniya.

  • Zargin Da Amurka Ta Yi Wa Sin Game Da Gwajin Nukiliya Ba Shi Da Tushe
  • Mu’amala Tsakanin Shugabannin Sin Da Amurka Tana Taka Muhimmiyar Rawa A Dangantakar Kasashen

Kazalika, wasu alkaluma da hukumar ta fitar a hukumance, sun nuna cewa, daga tsakanin 2021 zuwa 2026 NDLEA, a daukacin fadin kasar, ta yi kamen da ke da alaka da shan kayan mayen, da suka kai adadin dubu 77,792.

ADVERTISEMENT

Kamen ya hada da na dai-daikun shaharattun masu sayar da kayan maye   guda 28 da kuma wasu manyan jiga-jigan dilolin kayan maye, da suka shahara a duniya.

Bugu da kari, a dai tsakanin wadannan shekarun, NDLEA ta samu nasarar a gaban Kotu, na ganin an gurfanar tare da kuma yankewa wadanda aka kama da laifikasar, 14,225 hukunci, a gaban kotu.

LABARAI MASU NASABA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

Ta alakanta wannan sanarar ga babbar karfafa hadaka da ta samu daga bangaren Shari’ar kasar.

Wannan Jaridar, ta damu matuka,  kan kara samun lamuran da suka shafi, yin tu’ammali da kayan mayen a kasar, musamman ganin yadda dabi’ar ta zama tamkar ruwan dare, a tsakanin wasu matasan kasar duk da kokarin da NDLEA ke ci gaba da yi, na yakar dabi’ar.

Matasa dai, sune kashin bayan kowacce irin alumma, amma abin bakin ciki, su ne, kan gaba wajen yin dabi’ar inda hakan ke janyo wasu su haukace ko kuma shaye-sahyen, ya shafi lafiyarsu.

Bisa wani bincike da aka gudanar, ya nuna cewa, shiyyar Kudu Maso Gabas, musamman a jihohin Legas, Oyo, Ogun, da Ondo, nan ne ke kan gaba a yin dabi’ar, inda suke da kaso 24 a cikin dari, sai kuma Kudu Maso Kudu da ke da kaso 18.

Bugu da kari, a Arewa Maso Yanna kuwa, akasari an fi tu’ammali da codeine syrup, inda kuma a Arewa Maso Gabas, musamman a jihohin Gombe, Yobe, Adamawa, da Bauchi, nan ma lamarin, yayi kamari.

Butun na shan kayan mayen, abu ne, dai da zama tamkar gobarar Jeji, a fadin duniya, duba da alkaluman da ofishin majalisar dinkin duniya da ke yaki da shan kaya maye, ya fitar, inda alkaluman suka nuna cewa, akalla masu tu’ammali da kayan maye a 2020, sun kai miliyan 284.

Kazalika, a cikin wani rahoto da majalisar dinkin duniya ta fitar a 2022, ya ce, ana noman Tabar Wiwi, a kasashe 154 tare da kuma kayan maye na opium, da ake nomawa a kasashe  57.

Hakazalika, NDLEA ta sanar da cewa, daga cikin tan dubu 15,000 na nau’ukan kayan maye da ta kwace, a shekaru biyar da suka wuce, sama da kaso 75, duk na Tabawar Wiwi ne.

Wannan Jaridar na da yakin cewa, musamman bisa dogaro kan wani bincike da aka gudanar, ya nuna cewa, shan kayan maye, musamman cocaine, na bai wa masu sha, aikata manyan laifuka.

Misali, irin ayyukan rashin imani da ‘yan ta’addar kungiyar Boko Haram da masu garkuwa da mutane ke aikatawa, suna da nasaba sham muggan kayan maye.

Akwai dai, matukar bukatar mahukunta a kasar nan, su kara daura damarar kawo karshen wannan mummunar dabi’ar.

Idan za a iya tunawa, a 2024 musamman kan aikin da majalisar dattawa ke yi, na yiwa kundin tsarin mulkin kasar garanbawul, ta bayar da shawara da a samar da wata doka da za ta bayar da damar, yanke hukunci, ga masu safarar miyagun kwayoyi, musamman hukuncin, ya kasance na kisa.

Idan kuma ba  hukuncin kisa ba, a yiwa masu safarar tsatsaruan hukunci na  zaman gidan kaso daga shekaru 15 25, ba tare da cin wata tara ba.

Wani karin abin takaicin, a duk kokacin da ake gudanar da zagayowar ranar yaki da shan kayan maye ta duniya, za a ga, mawaka da dauko domin gangamin wayar kai kan yakin, suma a wajen taron, suna ta faman shan kayan mayen a bainar jama’a, inda su kuma jami’an tsaro, basa taka masu birki.

Karin wani abin bakin cikin shi ne, yadda ake yin amfani da Tashohin Jiragen Ruwan kasar, wajen yin safarar muggan kayan maye.

A ra’ayinmu, muna ganin akwai matukar bukatar a samar da kyawawan dabaru da limantar wa alumma, kuma hukumomin kasar su kara jajircewa, wajen yakar dabi’ar a kasar.

Maye
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe
Maye
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

May 15, 2026
Next Post
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Manoma Da Makiyaya Sun Kulla Yarjejeniyar Zaman Lafiya A Filato

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.