ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 8: Haƙuri Da Sadaukarwa Domin Rabauta Ta Har Abada

by Nuhu Ubale Ibrahim
5 months ago
Ramadan

A cikin watan Ramalana muna koyon haƙuri wajen cimma kyawawan burace-buracenmu. Ramalana makaranta ce ta juriya da sadaukarwa. Yana koya mana cewa babu damuwa, babu aibi, babu hasara idan mutum ya bar wasu abubuwan more rayuwa na ɗan lokaci domin neman jin daɗi na har abada.

Azumi ba abu ne sauƙi ba, yana buƙatar ka bar abin da kake so kuma kake iya samu, domin samun wani matsayi a wurin Allah. Mumini yana barin abinci, da ruwa da sauran abubuwan jin daɗi ne saboda Allah. Wannan barin da ya yi, ba rashi ba ne, face jarabawa ce da za ta haifar da riba mai girma a duniya da lahira. Manzon Allah (S.A.W ) ya bayyana girman ladan azumi da cewa mutum na iya samun gafarar Allah ta dalilinsa, idan ya yi shi da imani da neman lada. Azumi yana kankare zunubai, yana ɗaukaka darajoji, yana tsarkake zuciya.

  • Darussa Daga Ramadan Na 6: Girmama Ni’ima Da Gujewa Almubazzaranci A Ramalana
  • Darussa Daga Ramadan Na 5: Tsare Gaɓɓai Daga Saɓo

Ka lura da girman ladan azumin rana guda kacal. Ya zo a cikin Sunan na an-Nasa’i cewa Manzon Allah (S.A.W) ya ce:” Duk wanda ya yi azumin rana ɗaya domin Allah,to, Allah zai nisanta fuskarsa daga wuta tsawon tafiyar shekara saba’in”
Wannan hadisi Muhammad Nasiruddin al-Albani ya inganta shi.

ADVERTISEMENT

Ka yi tunani: rana ɗaya kacal! Amma ladanta kariya ce daga wuta tsawon tafiya mai nisa ƙwarai. Wannan yana nuna cewa abin da muke gani ƙarami a duniya, a wurin Allah yana da girma matuƙa idan ya kasance da ikhlasi.

Ramalana yana koya mana darasin jinkirta jin daɗi. Watau ka bar jin daɗin yanzu domin ka samu mafi girma a gaba. Wannan hikima ce da ta shafi duniya ma; duk wanda ya iya haƙuri, ya jure wahala kaɗan domin manufa mai girma, shi ne yake kaiwa ga nasara. Mumini yana barin jin daɗi na wucin gadi domin tsira da rabauta a ranar Lahira. Yana jure yunwa domin cikewar rahama. Yana jure ƙishirwa domin shan ruwan Aljanna. Yana jure gajiya domin dawwamammen hutu.

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

Haƙuri a Ramalana ba kawai haƙurin yunwa ba ne, har ma haƙuri ne a kan ibada, da haƙuri a kan nisantar saɓo, da haƙuri a kan kyautatawa mutane, da haƙuri a kan gyaran hali.

Idan muka fita daga Ramalana da wannan darasi, to za mu zama masu iya jure wahalhalun rayuwa domin manyan manufofi. Za mu iya barin haram domin halal, za mu iya barin ƙarya domin gaskiya, za mu iya barin son zuciya domin yardar Allah.

Allah Ya ba mu haƙuri na gaskiya, Ya karɓi azuminmu, Ya nisanta mu daga wuta, Ya kuma sa mu cikin masu rabauta a ranar Lahira. Amin.

Abu Razina Nuhu Ubale Ibrahim Paki

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa
Fatawa

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

June 21, 2026
Next Post
Sin Na Bibiyar Halin Da Ake Ciki Yayin Da Zaman Tankiya Ke Karuwa Tsakanin Amurka Da Iran

Sin Na Bibiyar Halin Da Ake Ciki Yayin Da Zaman Tankiya Ke Karuwa Tsakanin Amurka Da Iran

LABARAI MASU NASABA

Ramadan

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

July 27, 2026
Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

July 27, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

July 27, 2026
Ramadan

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
Ramadan

WAFU B 2026: Nijeriya Ta Doke Ghana Da Ci 4-2 A Wasan Farko

July 27, 2026
An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

July 27, 2026
Ramadan

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.