ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 8: Haƙuri Da Sadaukarwa Domin Rabauta Ta Har Abada

by Nuhu Ubale Ibrahim
3 months ago
Ramadan

A cikin watan Ramalana muna koyon haƙuri wajen cimma kyawawan burace-buracenmu. Ramalana makaranta ce ta juriya da sadaukarwa. Yana koya mana cewa babu damuwa, babu aibi, babu hasara idan mutum ya bar wasu abubuwan more rayuwa na ɗan lokaci domin neman jin daɗi na har abada.

Azumi ba abu ne sauƙi ba, yana buƙatar ka bar abin da kake so kuma kake iya samu, domin samun wani matsayi a wurin Allah. Mumini yana barin abinci, da ruwa da sauran abubuwan jin daɗi ne saboda Allah. Wannan barin da ya yi, ba rashi ba ne, face jarabawa ce da za ta haifar da riba mai girma a duniya da lahira. Manzon Allah (S.A.W ) ya bayyana girman ladan azumi da cewa mutum na iya samun gafarar Allah ta dalilinsa, idan ya yi shi da imani da neman lada. Azumi yana kankare zunubai, yana ɗaukaka darajoji, yana tsarkake zuciya.

  • Darussa Daga Ramadan Na 6: Girmama Ni’ima Da Gujewa Almubazzaranci A Ramalana
  • Darussa Daga Ramadan Na 5: Tsare Gaɓɓai Daga Saɓo

Ka lura da girman ladan azumin rana guda kacal. Ya zo a cikin Sunan na an-Nasa’i cewa Manzon Allah (S.A.W) ya ce:” Duk wanda ya yi azumin rana ɗaya domin Allah,to, Allah zai nisanta fuskarsa daga wuta tsawon tafiyar shekara saba’in”
Wannan hadisi Muhammad Nasiruddin al-Albani ya inganta shi.

ADVERTISEMENT

Ka yi tunani: rana ɗaya kacal! Amma ladanta kariya ce daga wuta tsawon tafiya mai nisa ƙwarai. Wannan yana nuna cewa abin da muke gani ƙarami a duniya, a wurin Allah yana da girma matuƙa idan ya kasance da ikhlasi.

Ramalana yana koya mana darasin jinkirta jin daɗi. Watau ka bar jin daɗin yanzu domin ka samu mafi girma a gaba. Wannan hikima ce da ta shafi duniya ma; duk wanda ya iya haƙuri, ya jure wahala kaɗan domin manufa mai girma, shi ne yake kaiwa ga nasara. Mumini yana barin jin daɗi na wucin gadi domin tsira da rabauta a ranar Lahira. Yana jure yunwa domin cikewar rahama. Yana jure ƙishirwa domin shan ruwan Aljanna. Yana jure gajiya domin dawwamammen hutu.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

Haƙuri a Ramalana ba kawai haƙurin yunwa ba ne, har ma haƙuri ne a kan ibada, da haƙuri a kan nisantar saɓo, da haƙuri a kan kyautatawa mutane, da haƙuri a kan gyaran hali.

Idan muka fita daga Ramalana da wannan darasi, to za mu zama masu iya jure wahalhalun rayuwa domin manyan manufofi. Za mu iya barin haram domin halal, za mu iya barin ƙarya domin gaskiya, za mu iya barin son zuciya domin yardar Allah.

Allah Ya ba mu haƙuri na gaskiya, Ya karɓi azuminmu, Ya nisanta mu daga wuta, Ya kuma sa mu cikin masu rabauta a ranar Lahira. Amin.

Abu Razina Nuhu Ubale Ibrahim Paki

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Next Post
Sin Na Bibiyar Halin Da Ake Ciki Yayin Da Zaman Tankiya Ke Karuwa Tsakanin Amurka Da Iran

Sin Na Bibiyar Halin Da Ake Ciki Yayin Da Zaman Tankiya Ke Karuwa Tsakanin Amurka Da Iran

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.