ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Obasanjo Ya Kafa Kwamitin Bincike Akai Na, Amma Bai Same Ni Da Laifi Ba — Atiku

by Abubakar Sulaiman
3 months ago

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa tsohon shugabansa, Olusegun Obasanjo, ya taɓa kafa wani babban kwamiti domin bincikensa a lokacin da yake kan mulki, amma binciken bai gano wata alamar cin hanci ko rashawa a kansa ba. Atiku ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi a shirin Prime Time Special na gidan talabijin na ARISE News a ranar Laraba.

A cewarsa, an kafa kwamitin ne ƙarƙashin tsohon Babban Lauyan Tarayya, Bayo Ojo (SAN), inda ya haɗa da fitattun mutane kamar tsohon shugaban Hukumar EFCC kuma mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro a yanzu, Nuhu Ribadu, da kuma tsohon ministan Babban Birnin Tarayya kuma tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai.

Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo

ADVERTISEMENT

Obasanjo Zai Zuba Jarin Dala Miliyan 700 A Kamaru

Atiku ya ce duk da cewa yana da kariya ta kundin tsarin mulki a matsayin mataimakin shugaban ƙasa a lokacin, ya amince a cire wannan kariya domin a gudanar da binciken. Ya ce jami’an kwamitin sun zo ofishinsa da umarnin shugaban ƙasa na su bincike shi, kuma ya basu damar yin hakan ba tare da wata tangarɗa ba.

LABARAI MASU NASABA

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

Ya jaddada cewa sakamakon binciken ya wanke shi daga duk wani zargi, yana mai cewa babu abin da aka samu a kansa. Ya ƙara da cewa zarge-zargen rashawa da ake alaƙanta shi da su tsawon lokaci ba su da hujja, illa kawai siyasa ce ke haddasa su.

Atiku ya bayyana lamarin a matsayin abin da bai taba faruwa ba, inda shugaban ƙasa ya ba da umarnin binciken mataimakinsa da ke da kariya ta doka, yana mai cewa wannan shi ne karo na farko da yake bayyana hakan a bainar jama’a.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa
  • Abubakar Sulaiman
    Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata
  • Abubakar Sulaiman
    Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

MASU ALAKA

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Manyan Labarai

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft
Labarai

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Next Post
Ce-ce-ku-ce Kan Batun Biyan Bashin Naira Tiriliyan 3.3 Na Kuɗin Lantarki

Ce-ce-ku-ce Kan Batun Biyan Bashin Naira Tiriliyan 3.3 Na Kuɗin Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.