ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Obasanjo Ya Kafa Kwamitin Bincike Akai Na, Amma Bai Same Ni Da Laifi Ba — Atiku

by Abubakar Sulaiman
3 months ago

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa tsohon shugabansa, Olusegun Obasanjo, ya taɓa kafa wani babban kwamiti domin bincikensa a lokacin da yake kan mulki, amma binciken bai gano wata alamar cin hanci ko rashawa a kansa ba. Atiku ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi a shirin Prime Time Special na gidan talabijin na ARISE News a ranar Laraba.

A cewarsa, an kafa kwamitin ne ƙarƙashin tsohon Babban Lauyan Tarayya, Bayo Ojo (SAN), inda ya haɗa da fitattun mutane kamar tsohon shugaban Hukumar EFCC kuma mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro a yanzu, Nuhu Ribadu, da kuma tsohon ministan Babban Birnin Tarayya kuma tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai.

Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo

ADVERTISEMENT

Obasanjo Zai Zuba Jarin Dala Miliyan 700 A Kamaru

Atiku ya ce duk da cewa yana da kariya ta kundin tsarin mulki a matsayin mataimakin shugaban ƙasa a lokacin, ya amince a cire wannan kariya domin a gudanar da binciken. Ya ce jami’an kwamitin sun zo ofishinsa da umarnin shugaban ƙasa na su bincike shi, kuma ya basu damar yin hakan ba tare da wata tangarɗa ba.

LABARAI MASU NASABA

Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata

Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran

Ya jaddada cewa sakamakon binciken ya wanke shi daga duk wani zargi, yana mai cewa babu abin da aka samu a kansa. Ya ƙara da cewa zarge-zargen rashawa da ake alaƙanta shi da su tsawon lokaci ba su da hujja, illa kawai siyasa ce ke haddasa su.

Atiku ya bayyana lamarin a matsayin abin da bai taba faruwa ba, inda shugaban ƙasa ya ba da umarnin binciken mataimakinsa da ke da kariya ta doka, yana mai cewa wannan shi ne karo na farko da yake bayyana hakan a bainar jama’a.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Enekweci Ne Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya A Wasannin Commonwealth Na Bana
  • Abubakar Sulaiman
    Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi
  • Abubakar Sulaiman
    Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC
  • Abubakar Sulaiman
    Mutane 600 Ne Kacal Suka Ci Jarabawar Ɗaukar Malaman Firamare Daga Cikin 8,000

MASU ALAKA

Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata
Labarai

Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata

July 5, 2026
Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran
Labarai

Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran

July 5, 2026
Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

July 5, 2026
Next Post
Ce-ce-ku-ce Kan Batun Biyan Bashin Naira Tiriliyan 3.3 Na Kuɗin Lantarki

Ce-ce-ku-ce Kan Batun Biyan Bashin Naira Tiriliyan 3.3 Na Kuɗin Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata

Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata

July 5, 2026
Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran

Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran

July 5, 2026
Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

July 5, 2026
LeBron James Zai Bar Los Angeles Lakers 

LeBron James Zai Bar Los Angeles Lakers 

July 5, 2026
Enekweci Ne Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya A Wasannin Commonwealth Na Bana

Enekweci Ne Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya A Wasannin Commonwealth Na Bana

July 5, 2026
Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.