Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa tsohon shugabansa, Olusegun Obasanjo, ya taɓa kafa wani babban kwamiti domin bincikensa a lokacin da yake kan mulki, amma binciken bai gano wata alamar cin hanci ko rashawa a kansa ba. Atiku ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi a shirin Prime Time Special na gidan talabijin na ARISE News a ranar Laraba.
A cewarsa, an kafa kwamitin ne ƙarƙashin tsohon Babban Lauyan Tarayya, Bayo Ojo (SAN), inda ya haɗa da fitattun mutane kamar tsohon shugaban Hukumar EFCC kuma mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro a yanzu, Nuhu Ribadu, da kuma tsohon ministan Babban Birnin Tarayya kuma tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai.
Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo
Obasanjo Zai Zuba Jarin Dala Miliyan 700 A Kamaru
Atiku ya ce duk da cewa yana da kariya ta kundin tsarin mulki a matsayin mataimakin shugaban ƙasa a lokacin, ya amince a cire wannan kariya domin a gudanar da binciken. Ya ce jami’an kwamitin sun zo ofishinsa da umarnin shugaban ƙasa na su bincike shi, kuma ya basu damar yin hakan ba tare da wata tangarɗa ba.
Ya jaddada cewa sakamakon binciken ya wanke shi daga duk wani zargi, yana mai cewa babu abin da aka samu a kansa. Ya ƙara da cewa zarge-zargen rashawa da ake alaƙanta shi da su tsawon lokaci ba su da hujja, illa kawai siyasa ce ke haddasa su.
Atiku ya bayyana lamarin a matsayin abin da bai taba faruwa ba, inda shugaban ƙasa ya ba da umarnin binciken mataimakinsa da ke da kariya ta doka, yana mai cewa wannan shi ne karo na farko da yake bayyana hakan a bainar jama’a.















Discussion about this post