Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, na dab da zama ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar (NDC) bayan da ya kasance shi kaɗai ya sayi fom ɗin nuna sha’awa da takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar gabanin zaɓen shekarar 2027.
Wannan ci gaba na zuwa ne yayin da ake samun ƙarin rarrabuwar kai a tsakanin jam’iyyun adawa, bayan rushewar haɗakar ADC da ta haɗa Obi, tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar, da tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso.
Jam’iyyar NDC ta tabbatar da cewa ta rufe sayar da fom ɗin takarar shugaban ƙasa a ranar Lahadi, yayin da ta ƙara wa’adin sayar da fom ga masu neman takarar gwamna, majalisar dattawa, majalisar wakilai da majalisun jihohi da mako guda.
Majiyoyin jam’iyyar sun ce yanzu Obi na iya zama ɗan takarar na NDC ba tare da hamayya ba, ganin cewa babu wani ɗan takarar shugaban ƙasa da ya sayi fom ɗin.















Discussion about this post