Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya zaɓi tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, a matsayin abokin takararsa a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
Obi ya sanar da hakan ne a ranar Asabar yayin jawabinsa na karɓar takara bayan da aka tabbatar da shi a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar a wani taro na musamman da aka gudanar a Abuja.
Tsohon gwamnan Jihar Anambra ya zama ɗan takara shi kaɗai a zaɓen fidda-gwani na jam’iyyar da aka gudanar a ranar 29 ga watan Mayu, 2026.
An amince da takararsa ne bayan wani ƙuduri da Sanata Victor Umeh ya gabatar, yayin da tsohon Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Ovie Omo-Agege, ya mara masa baya.
Bayan tabbatar da takarar, jagoran jam’iyyar NDC, Sanata Seriake Dickson, da Shugaban Jam’iyyar na Ƙasa, Sanata Cleopas Moses Zuwoghe, sun miƙa masa tutar jam’iyyar.















Discussion about this post