Jam’iyyar PDP ƙarƙashin jagorancin Tanimu Turaki ta amince da tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Ebele Jonathan, domin tsayawa takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar.
Da yake magana bayan kammala tantance ‘yan takara a Abuja, shugaban kwamitin tantancewar kuma tsohon gwamnan Jihar Neja, Babangida Aliyu, ya ce, an amince Jonathan ya yi takara ba tare da wata tantancewa ba saboda irin manyan muƙaman gwamnati da ya taɓa riƙewa.
Aliyu ya ce: “Jam’iyyar ta amince wa wani mai neman takarar shugaban ƙasa yin takara kai tsaye ba tare da wata tantancewa ba. Kamar yadda na faɗa tun farko, ya kasance mataimakin gwamna, daga baya ya zama gwamna, mataimakin shugaban ƙasa sannan shugaban ƙasa, saboda haka ba mu ga wani abu da ke buƙatar tantancewa ba.
“Saboda haka, jam’iyyar ta amince masa. Ma’ana, an ayyana shi kuma an amince da shi a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na PDP a zaɓe mai zuwa, kuma shi ne tsohon Shugaban Ƙasa Jonathan.”















Discussion about this post