A kwanan nan, wani rahoton “Binciken Jin Ra’ayoyi na Matasan Afirka na shekarar 2026” da gidauniyar Ichikowitz Family ta kasar Afirka ta Kudu ta fitar, ya nuna cewa a mahangar matasan Afirka, tasirin kasar Sin mai kyau a nahiyar na ci gaba da karuwa, kuma matsayin kasar Sin na muhimmiyar abokiyar hadin gwiwa a nahiyar yana dada samun tagomashi.
An kaddamar da yin binciken ne a watan Maris na bana, inda ya karade kasashen Afirka 16 tare da tattara ra’ayoyin matasa kusan 5,000 masu shekaru tsakanin 18 zuwa 24.
Binciken ya nuna cewa, daga cikin wadanda suka yi amannar cewa kasar Sin na da tasiri a kasarsu, kashi 95 na matasan na Afirka sun ba da kyakkyawar shaida a kan tasirin kasar Sin a matakin kasa da kasa, wanda hakan ya nuna samun karuwar kashi 18 cikin dari idan aka kwatanta da shekarar 2022. Wadannan alkaluma na nuna cewa tasirin kasar Sin a kan matasan Afirka na ci gaba da karuwa.
Dangane da fahimtar dangantaka tsakanin Sin da kasashen Afirka kuwa, kashi 95 cikin dari na matasan Afirka da aka ji ra’ayoyinsu suna kallon kasar Sin a matsayin abokiyar hadin gwiwa tagari.Rahoton ya nuna cewa matasan Afirka sun fi mayar da hankali kan sakamako na zahiri da ake samu daga hadin gwiwa.
Kashi 55 cikin dari na wadanda suka bayyana ra’ayoyin kuma sun nuna cewa, ya kamata kasashen Afirka su ba da fifiko ga abokan hulda da za su iya samar masu da damar kasuwanci da zuba jari. Wanda ya shirya binciken, Ivor Ichikowitz, ya ce, “Kasar Sin na samun amincewar matasan da za su nuna yanke hukunci kan makomar Afirka.” (Abdulrazaq Yahuza Jere)














