ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

by Shehu Yahaya and Sulaiman
3 months ago
Uba Sani

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya saki fursunoni 97 da ke Gidan gyaran hali na Kaduna, inda ya ba su ‘yanci tare da tanadar musu tallafin kuɗi da damar koyon sana’o’i domin fara sabuwar rayuwa.

Da yake jawabi a wajen bikin da aka gudanar a gidan gyaran halin Kaduna, Gwamna Uba Sani ya bayyana cewa ranar 12 ga Yuni wata rana ce mai muhimmanci a tarihin Nijeriya, wadda ke tunatar da al’umma irin sadaukarwar da jaruman dimokuraɗiyya suka yi wajen tabbatar da mulkin farar hula da ‘yancin jama’a.

Gwamnan ya ce sakin fursunonin ya biyo bayan amfani da ikon afuwa da kundin tsarin mulkin ƙasa ya ba shi, bayan shawarwarin Kwamitin ba da Afuwa na Jihar Kaduna wanda ya tantance waɗanda suka cancanci cin gajiyar shirin.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, shirin ya haɗa da sakin wasu gaba ɗaya, rage wa wasu hukunci da kuma biyan tara ga wasu domin su samu damar komawa cikin al’umma.

Uba Sani, wanda ya kasance cikin masu fafutukar neman dimokuraɗiyya a baya, ya yi jinjina ga marigayi Cif MKO Abiola, Cif Gani Fawehinmi, Dakta Beko Ransome-Kuti, Hajiya Kudirat Abiola da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, tare da sauran jaruman da suka sadaukar da rayuwarsu wajen tabbatar da dimokuraɗiyya a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Ya ce sadaukarwar da suka yi ta nuna cewa ‘yanci da dimokuraɗiyya abubuwa ne da ya kamata a ci gaba da karewa da bunƙasa su domin amfanin al’umma.

Domin tabbatar da cewa waɗanda aka saki sun samu kyakkyawar makoma, gwamnan ya sanar da bayar da tallafin kuɗi ga dukkan fursunonin 97 da aka yi wa afuwa, tare da ba su damar shiga cibiyoyin koyon sana’o’i na gwamnatin jihar da ke Soba, Rigachikun da Samaru-Kataf domin koyon sana’o’in da za su dogara da kansu.

Ya jaddada cewa gwamnatin sa ta yi imani da gyaran hali, ba wai hukunci kaɗai ba, yana mai cewa kowa na da damar sauya rayuwarsa idan aka ba shi dama.

Gwamnan ya kuma yi kira ga sarakuna, malamai, shugabannin al’umma da sauran jama’a da su karɓi waɗanda aka saki hannu bibbiyu tare da taimaka musu wajen sake shiga rayuwar yau da kullum.

A wani mataki na tallafawa gyaran hali, Gwamna Uba Sani ya amince da bayar da motar aiki ga Hukumar Kula da gidajen gyaran hali ta Nijeriya reshen jihar Kaduna, tare da ba da kayan aikin lafiya da magunguna domin inganta kula da lafiyar fursunoni.

Tun da farko, Babban Lauyan Jihar Kaduna kuma Kwamishinan Shari’a, Barista James Kanyip, ya bayyana matakin a matsayin wata alama ta shugabanci mai tausayi da hangen nesa na Gwamna Uba Sani.

Ya ce ikon afuwa wata muhimmiyar hanya ce ta haɗa adalci da jin ƙai, tare da taimakawa wajen rage cunkoso a gidajen gyaran hali da kuma bai wa mutane damar sake gina rayuwarsu.

Uba Sani
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamna Uba Sani Ya Yi Jimamin Rasuwar Dan Jarida Jafaru Yakubu Maitama
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamnatin Kaduna Ta Fara Rabon Takin Zamani Kyauta Ga Manoma 150,000
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Zaka Iya Sayar da Takin Gwamnati Ka Sayawa Iyalinka Kaji — Imam Nuradden
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Rashin Tsaro: ACI Zata Kira Taron Gaggawa Na Masu Ruwa Da Tsaki A Kaduna
Uba Sani
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.