ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

by Shehu Yahaya and Sulaiman
1 month ago
Uba Sani

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya saki fursunoni 97 da ke Gidan gyaran hali na Kaduna, inda ya ba su ‘yanci tare da tanadar musu tallafin kuɗi da damar koyon sana’o’i domin fara sabuwar rayuwa.

Da yake jawabi a wajen bikin da aka gudanar a gidan gyaran halin Kaduna, Gwamna Uba Sani ya bayyana cewa ranar 12 ga Yuni wata rana ce mai muhimmanci a tarihin Nijeriya, wadda ke tunatar da al’umma irin sadaukarwar da jaruman dimokuraɗiyya suka yi wajen tabbatar da mulkin farar hula da ‘yancin jama’a.

Gwamnan ya ce sakin fursunonin ya biyo bayan amfani da ikon afuwa da kundin tsarin mulkin ƙasa ya ba shi, bayan shawarwarin Kwamitin ba da Afuwa na Jihar Kaduna wanda ya tantance waɗanda suka cancanci cin gajiyar shirin.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, shirin ya haɗa da sakin wasu gaba ɗaya, rage wa wasu hukunci da kuma biyan tara ga wasu domin su samu damar komawa cikin al’umma.

Uba Sani, wanda ya kasance cikin masu fafutukar neman dimokuraɗiyya a baya, ya yi jinjina ga marigayi Cif MKO Abiola, Cif Gani Fawehinmi, Dakta Beko Ransome-Kuti, Hajiya Kudirat Abiola da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, tare da sauran jaruman da suka sadaukar da rayuwarsu wajen tabbatar da dimokuraɗiyya a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Ya ce sadaukarwar da suka yi ta nuna cewa ‘yanci da dimokuraɗiyya abubuwa ne da ya kamata a ci gaba da karewa da bunƙasa su domin amfanin al’umma.

Domin tabbatar da cewa waɗanda aka saki sun samu kyakkyawar makoma, gwamnan ya sanar da bayar da tallafin kuɗi ga dukkan fursunonin 97 da aka yi wa afuwa, tare da ba su damar shiga cibiyoyin koyon sana’o’i na gwamnatin jihar da ke Soba, Rigachikun da Samaru-Kataf domin koyon sana’o’in da za su dogara da kansu.

Ya jaddada cewa gwamnatin sa ta yi imani da gyaran hali, ba wai hukunci kaɗai ba, yana mai cewa kowa na da damar sauya rayuwarsa idan aka ba shi dama.

Gwamnan ya kuma yi kira ga sarakuna, malamai, shugabannin al’umma da sauran jama’a da su karɓi waɗanda aka saki hannu bibbiyu tare da taimaka musu wajen sake shiga rayuwar yau da kullum.

A wani mataki na tallafawa gyaran hali, Gwamna Uba Sani ya amince da bayar da motar aiki ga Hukumar Kula da gidajen gyaran hali ta Nijeriya reshen jihar Kaduna, tare da ba da kayan aikin lafiya da magunguna domin inganta kula da lafiyar fursunoni.

Tun da farko, Babban Lauyan Jihar Kaduna kuma Kwamishinan Shari’a, Barista James Kanyip, ya bayyana matakin a matsayin wata alama ta shugabanci mai tausayi da hangen nesa na Gwamna Uba Sani.

Ya ce ikon afuwa wata muhimmiyar hanya ce ta haɗa adalci da jin ƙai, tare da taimakawa wajen rage cunkoso a gidajen gyaran hali da kuma bai wa mutane damar sake gina rayuwarsu.

Uba Sani
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
Uba Sani
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba
  • Sulaiman
    An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI
  • Sulaiman
    Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya
  • Sulaiman
    Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

MASU ALAKA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Labarai

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci
Rahotonni

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Next Post
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

LABARAI MASU NASABA

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.