ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

by Shehu Yahaya and Sulaiman
8 hours ago
Uba Sani

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya saki fursunoni 97 da ke Gidan gyaran hali na Kaduna, inda ya ba su ‘yanci tare da tanadar musu tallafin kuɗi da damar koyon sana’o’i domin fara sabuwar rayuwa.

Da yake jawabi a wajen bikin da aka gudanar a gidan gyaran halin Kaduna, Gwamna Uba Sani ya bayyana cewa ranar 12 ga Yuni wata rana ce mai muhimmanci a tarihin Nijeriya, wadda ke tunatar da al’umma irin sadaukarwar da jaruman dimokuraɗiyya suka yi wajen tabbatar da mulkin farar hula da ‘yancin jama’a.

Gwamnan ya ce sakin fursunonin ya biyo bayan amfani da ikon afuwa da kundin tsarin mulkin ƙasa ya ba shi, bayan shawarwarin Kwamitin ba da Afuwa na Jihar Kaduna wanda ya tantance waɗanda suka cancanci cin gajiyar shirin.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, shirin ya haɗa da sakin wasu gaba ɗaya, rage wa wasu hukunci da kuma biyan tara ga wasu domin su samu damar komawa cikin al’umma.

Uba Sani, wanda ya kasance cikin masu fafutukar neman dimokuraɗiyya a baya, ya yi jinjina ga marigayi Cif MKO Abiola, Cif Gani Fawehinmi, Dakta Beko Ransome-Kuti, Hajiya Kudirat Abiola da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, tare da sauran jaruman da suka sadaukar da rayuwarsu wajen tabbatar da dimokuraɗiyya a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ya ce sadaukarwar da suka yi ta nuna cewa ‘yanci da dimokuraɗiyya abubuwa ne da ya kamata a ci gaba da karewa da bunƙasa su domin amfanin al’umma.

Domin tabbatar da cewa waɗanda aka saki sun samu kyakkyawar makoma, gwamnan ya sanar da bayar da tallafin kuɗi ga dukkan fursunonin 97 da aka yi wa afuwa, tare da ba su damar shiga cibiyoyin koyon sana’o’i na gwamnatin jihar da ke Soba, Rigachikun da Samaru-Kataf domin koyon sana’o’in da za su dogara da kansu.

Ya jaddada cewa gwamnatin sa ta yi imani da gyaran hali, ba wai hukunci kaɗai ba, yana mai cewa kowa na da damar sauya rayuwarsa idan aka ba shi dama.

Gwamnan ya kuma yi kira ga sarakuna, malamai, shugabannin al’umma da sauran jama’a da su karɓi waɗanda aka saki hannu bibbiyu tare da taimaka musu wajen sake shiga rayuwar yau da kullum.

A wani mataki na tallafawa gyaran hali, Gwamna Uba Sani ya amince da bayar da motar aiki ga Hukumar Kula da gidajen gyaran hali ta Nijeriya reshen jihar Kaduna, tare da ba da kayan aikin lafiya da magunguna domin inganta kula da lafiyar fursunoni.

Tun da farko, Babban Lauyan Jihar Kaduna kuma Kwamishinan Shari’a, Barista James Kanyip, ya bayyana matakin a matsayin wata alama ta shugabanci mai tausayi da hangen nesa na Gwamna Uba Sani.

Ya ce ikon afuwa wata muhimmiyar hanya ce ta haɗa adalci da jin ƙai, tare da taimakawa wajen rage cunkoso a gidajen gyaran hali da kuma bai wa mutane damar sake gina rayuwarsu.

Uba Sani
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Bayan Shehu Sani Ya Ƙalubalanci Zailani, Rikicin APC Ya Ƙara Zafi A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ya Dace ‘Yan Arewa Su Ƙara Marawa Tinubu Baya Domin Kammala Wa’adi Na Biyu — Shehu Sani
Uba Sani
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • Sulaiman
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

MASU ALAKA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
Labarai

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
Labarai

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Next Post
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.