Wani magidanci ya kai ƙarar matarsa a kotu, yana zargin cewa ta daina dafa masa abinci tare da dukansa duk lokacin da saɓani ya taso a tsakaninsu. Mutumin ya ce halin da yake ciki ya sa rayuwarsa ta zama cikin damuwa da rashin kwanciyar hankali.
Ya bayyana hakan ne yayin zaman sauraron ƙarar aurensu, inda ya roƙi kotu da ta shiga tsakaninsu domin kawo ƙarshen matsalolin da suka dabaibaye aurensu. A cewarsa, rikicin cikin gidan ya daɗe yana ƙara muni duk da ƙoƙarin sasanci da aka yi.
Magidancin ya ce matarsa ba kawai ta daina kulawa da shi ba ne, har ma tana kai masa hari idan sun samu rashin jituwa a kan al’amuran yau da kullum. Ya ƙara da cewa ya sha jurewa cikin fatan lamarin zai gyaru amma abin ya ci tura.
Lamarin ya janyo ce-ce-ku-ce, inda masu sharhi ke cewa cin zarafin cikin gida ba ya shafar mata kaɗai, domin maza ma na iya fuskantar irin wannan matsala a aure.















Discussion about this post