ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Yarda Da Sauran Abubuwan Da Ke Haifar Da Sabani Tsakanin Nijar Da Benin

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
8 months ago
Benin

A ranar Litinin ne gwamnatin Jamhuriyar Benin da ke Yammacin Afirka ta sanar da rufe ofishin jakadancinta da ke Yamai na Jamhuriyar Nijar, a wani abu da masana ke bayyanawa da tabarbarewar alaka tsakanin kasasashen biyu.

A cewar hukumomin kasar ta Benin, sun dauki matakin ne bayan wasu lamura da suka fi karfinsu, kodayake ba ta fitar da wani karin bayani a hukumance kan lamarin ba.

A nata bangare ita ma Jamhuriyar Nijar ta mayar da martani kan wannan mataki, in da ta umarci jami’in diflomasiyyar Benin ya saka hannu kan takardar dakatar da aiki, sannan ya bar kasar cikin sa’o’i 48.

ADVERTISEMENT

Lamarin ya faro ne tun bayan da hukumomin Benin suka dauki matakin korar shugaban hukumar leken asirin Nijar da ke birnin Cotonou da kwamishiniyar ‘yansanda da ke ofishin jakadancin Nijar a Cotonou bisa zargin aikata zagon kasa.

Inda a ranar 1 ga watan Janairu ma’aikatar harkokin wajen Nijar ta ayyana Seidou Imourana, babban jami’in Diplomasiyyar ofishin jakadancin Benin a matsayin wanda ba a bukatar zamansa a kasar, tare da umartarsa da ficewa daga kasar.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Ba wannan ne karo na farko da kasashen biyu makotan juna ke samun tsamin dangantar Diplomasiyya tsakaninsu ba.

Ko a shekarar 2024 Jamhuriyar Benin ta yi yunkurin dakatar da wani shirin Nijar na shimfida bututun mai zuwa kasashen waje, lamarin da ya sa gwamnatin Nijar ta ce za ta karkatar da aikin domin bi da kasar Chadi.

Kasashen biyu dai na zargin juna da aikata zagon-kasa, makonni bayan yunkurin juyin mulki a Benin da bai yi nasara ba, inda wasu kafafon yada labaran Benin suka zargi Nijar da hannu a kitsa juyin mulkin, kodayake babu tartibiyar hujjar da ta tabbatar da hakan.

Tun bayan juyin mulkin Nijar na watan Yulin 2023, aka rika samun sabani tsakanin kasashen biyu, masu kusanci da juna.

Tun bayan juyin mulkin Nijar na watan Yulin 2023, aka rika samun sabani tsakanin kasashen biyu, masu kusanci da juna.

 

Me ya janyo takaddamar?

Mutane da dama kan yi mamakin yadda kasashen biyu makusantan juna ke takun-saka tsakaninsu, kasancewarsu al’umma iri daya masu al’adu iri daya, to amma me ya janyo musu wannan takaddama?

Alkasoum Abdourahmane masanin siyasa da al’amuran yau da kullum a yankin Afirka ta Yamma da kasashen Sahel ya ce matsalar ta samo asali ne tun bayan juyin mulkin da aka samu a Jamhuriyar Nijar a 2023.

Masanin diflomasiyyar ya ce matsayar da Benin ta dauka na rashin goyon bayan juyin mulkin Nijar na daga cikin abubuwan da suka assasa matsalar.

‘Bayan juyin mulkin NIjar ta yanke duk wata hulda da kasashen Yamma, to amma ita Benin sai ma ta kara karfafa alakar kawancenta da kasashen musamman Faransa, wani abu da Nijar ke kallo a matsayin barazana gareta”, in ji shi.

Alkasoum Abdourahmane ya kara da cewa yadda Benin ta hada kai da Ecowas wajen yi wa Nijar barazana da yunkurin kai mata hari, shi ma ya taimaka wajen tabarbarewar alaka tsakanin kasashen biyu.

 

Wace illar tabarbarwar alakar ke janyo musu?

Alkassoum Abdourahmane ya ce rashin kyawun alaka tsakanin kasashen biyu na haifar musu mummunar illa, da ya ce tuni ta samu.

Masanin ya ce ta fuskar kasuwanci da tattalin arziki tabarbarewar alakar na haifar wa kasashen biyu mummunart asara.

”Kusan a iya cewa Jamhuriyar Benin ba ta da wata kasa abokiyar kasuwanci da take amfani da tasoshin jiragen ruwanta kamar Nijar, kuma akwai wasu kasashen Afirka kamar Najeriya da Chadi da ma Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, wadanda duka ta NIjar kayayyakinsu ke biyowa”.

Ya kara da cewa sakamakon tabarbarewar alakar kasashen biyu an daina sauke wa Nijar kaya a tashar ruwan ta Benin.

”Kuma hakan ya haifar wa kasashen biyu asarar makudan kudaden shiga”, in ji shi.

Haka ma wasu masanan na ganin cewa rashin kyawun alaka tsakanin kasashen biyu na shafar yakin da suke yi da kungiyoyin masu aikata laifuka a cikin kasashen biyu da ke makwabtaka da juna.

”Kuma wannan na daga cikin manyan illolin da wannan takun saka zai haifar wa kasashen biyu”, a cewar Alkassoum.

Ya kara da cewa akwai iyakokin kasashe uku zuwa hudu a kan iyakar kasashen.

”Akwai iyakar Nijar da Benin da kuma Najeriya, haka ma akwai iyakar Benin da NIjar da kuma Burkina Faso, kuma rashin hadin kan kasashen zai shafi aikin tsaron hadin gwiwa a kan iyakokin”, kamar yadda ya bayyana.

 

Me ya kamata kasashen biyu su yi?

Abdollay Mustafa masanin harkokin diplosamiiya a jamhuriyar Nijar ya ce abinda ya kamata kasashen biyu su yi shi ne shugabannin su zauna wuri guda domin warware matsalar.

”Ya kamata shugabannin kasshen biyu su zauna su fahimci juna tsakaninsu da Allah, idan ana batun Diplomasiyya sai an kawo batun yarda da juan an kuma kawar da zargi”, in ji shi.

Ahmadou Dankware mai sharhi kan al’amuran yau da kullum a Nijar ya kuma shaida wa BBC cewa ya kamata shugabannin kasashen biyu su kalli al’umomin da ke wahala a cikin wannan al’amari.

”Yana da kyau shugabannin biyu su fahimci cewa duka al’umominsu na cikin wani kangi na wahala sakamakon wannan matsala, domin warware matsalar, tun da ai ko yaki ma ana yin sulhu”, kamar yadda ya yi karin haske.

Alkassoum Abdurrahman ya ce babu wata hanya da ta fi da lalama wajen warware matsaloli.

”Ya kamata kasashen biyu su zauna su cire mummunan zato da zargi tsakaninsu, domin magance wannan matsalar da ke janyo musu asara ta fuskar tattalin arziki da tsaro”, in ji shi.

Benin
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas
Benin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Wang Yi Ya Yi Tsokaci Dangane Da Dalilan Dadaddiyar Al’adar Ziyarar Da Ministocin Harkokin Wajen Sin Ke Fara Yi A Afirka A Duk Shekara

Wang Yi Ya Yi Tsokaci Dangane Da Dalilan Dadaddiyar Al’adar Ziyarar Da Ministocin Harkokin Wajen Sin Ke Fara Yi A Afirka A Duk Shekara

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.