ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

REA Da NCK Sun Ƙulla Yarjejeniya Da Jigawa Don Samar da Wutar Lantarki

by Abubakar Sulaiman
1 day ago
Jigawa

Hukumar Samar da Wutar Lantarki a Karkara (REA) ta sanar da cewa ta rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna (MoU) tare da Gwamnatin Jihar Jigawa, Nigerian Commodity Exchange (NCX) da kamfanin Astound Power Limited domin samar da wutar lantarki mai ƙarfin megawatt 7 (MW 7). An sanya hannu kan yarjejeniyar ne a yayin Taron Zuba Jari na Jigawa (J-Invest 2026), inda za ta tallafa wa haɗin gwuiwar gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu a cibiyoyin masana’antun noma guda bakwai da ke jihohin Jigawa, da Taraba, da Kaduna, Kebbi, da Ekiti, da Osun da Ebonyi.

REA ta bayyana cewa, a ƙarƙashin yarjejeniyar za ta gina kayayyakin samar da wutar lantarki domin tallafa wa tsarin ban ruwa da cibiyoyin sarrafa amfanin gona. Haka kuma, NCX za ta riƙa bai wa manoma da masu tara amfanin gona da suka cika ƙa’idoji takardun shaidar ajiya na rumbunan ajiyar kayayyaki da ke ƙarƙashin tsarin NCX, domin sauƙaƙa fitar da amfanin gona zuwa ƙasashen waje.

Da yake jawabi yayin sanya hannu kan yarjejeniyar, Manajan Daraktan REA, Dakta Abba Aliyu, ya ce ingantacciyar wutar lantarki na daga cikin manyan abubuwan da ke jawo masu zuba jari, da bunƙasa masana’antu da kuma samar da ayyukan yi a Nijeriya. Ya bayyana cewa haɗa makamashi mai tsafta da aikin noma zai ƙara ƙarfafa samar da wadataccen abinci, da samar da ayyukan yi masu ɗorewa da kuma ƙara darajar tattalin arziƙin manoma da al’ummomin karkara.

ADVERTISEMENT

Dakta Aliyu ya ƙara da cewa makamashi shi ne ginshiƙin ci gaban kasuwanci da bunƙasar al’umma, yana mai jaddada cewa zuba jari na bin inda ake da damarmaki da kuma amincewa da tsarin gwamnati.

Ya ce ɗaya daga cikin manyan saƙonnin da gwamnati za ta iya isarwa ga masu zuba jari shi ne nuna ƙudirin samar da yanayin da kasuwanci zai bunƙasa. Taron J-Invest 2026 ya haɗa masu tsara manufofi, da masu zuba jari, da abokan hulɗar ci gaba da shugabannin kamfanoni masu zaman kansu domin tattauna hanyoyin bunƙasa tattalin arziƙin Jihar Jigawa, yayin da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya buɗe taron a hukumance.

LABARAI MASU NASABA

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Jigawa
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi
  • Abubakar Sulaiman
    Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC
  • Abubakar Sulaiman
    Mutane 600 Ne Kacal Suka Ci Jarabawar Ɗaukar Malaman Firamare Daga Cikin 8,000
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnan Kano Ya Buƙaci EFCC, ICPC Su Sa Ido Kan Rabon Tallafin Taki

MASU ALAKA

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036
Labarai

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
Labarai

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Next Post
Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas

Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas

LABARAI MASU NASABA

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.