ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

REA Da NCK Sun Ƙulla Yarjejeniya Da Jigawa Don Samar da Wutar Lantarki

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago
Jigawa

Hukumar Samar da Wutar Lantarki a Karkara (REA) ta sanar da cewa ta rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna (MoU) tare da Gwamnatin Jihar Jigawa, Nigerian Commodity Exchange (NCX) da kamfanin Astound Power Limited domin samar da wutar lantarki mai ƙarfin megawatt 7 (MW 7). An sanya hannu kan yarjejeniyar ne a yayin Taron Zuba Jari na Jigawa (J-Invest 2026), inda za ta tallafa wa haɗin gwuiwar gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu a cibiyoyin masana’antun noma guda bakwai da ke jihohin Jigawa, da Taraba, da Kaduna, Kebbi, da Ekiti, da Osun da Ebonyi.

REA ta bayyana cewa, a ƙarƙashin yarjejeniyar za ta gina kayayyakin samar da wutar lantarki domin tallafa wa tsarin ban ruwa da cibiyoyin sarrafa amfanin gona. Haka kuma, NCX za ta riƙa bai wa manoma da masu tara amfanin gona da suka cika ƙa’idoji takardun shaidar ajiya na rumbunan ajiyar kayayyaki da ke ƙarƙashin tsarin NCX, domin sauƙaƙa fitar da amfanin gona zuwa ƙasashen waje.

Da yake jawabi yayin sanya hannu kan yarjejeniyar, Manajan Daraktan REA, Dakta Abba Aliyu, ya ce ingantacciyar wutar lantarki na daga cikin manyan abubuwan da ke jawo masu zuba jari, da bunƙasa masana’antu da kuma samar da ayyukan yi a Nijeriya. Ya bayyana cewa haɗa makamashi mai tsafta da aikin noma zai ƙara ƙarfafa samar da wadataccen abinci, da samar da ayyukan yi masu ɗorewa da kuma ƙara darajar tattalin arziƙin manoma da al’ummomin karkara.

ADVERTISEMENT

Dakta Aliyu ya ƙara da cewa makamashi shi ne ginshiƙin ci gaban kasuwanci da bunƙasar al’umma, yana mai jaddada cewa zuba jari na bin inda ake da damarmaki da kuma amincewa da tsarin gwamnati.

Ya ce ɗaya daga cikin manyan saƙonnin da gwamnati za ta iya isarwa ga masu zuba jari shi ne nuna ƙudirin samar da yanayin da kasuwanci zai bunƙasa. Taron J-Invest 2026 ya haɗa masu tsara manufofi, da masu zuba jari, da abokan hulɗar ci gaba da shugabannin kamfanoni masu zaman kansu domin tattauna hanyoyin bunƙasa tattalin arziƙin Jihar Jigawa, yayin da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya buɗe taron a hukumance.

LABARAI MASU NASABA

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Jigawa
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Wasiƙar Trump Ba Za Ta Ceto Tinubu Daga Faduwa Zaɓe Ba – Jam’iyyar ADC
  • Abubakar Sulaiman
    Amurka Ta Kakaba Harajin Kaso 12.5% A Kan kayayyakin Nijeriya
  • Abubakar Sulaiman
    NAFDAC Ta Kama Jabun Giya, Gurbataccen Abinci Da Motocin Man Kalanzir
  • Abubakar Sulaiman
    Shari’ar Malami Ba Za Ta Dakatar Da Burinsa Na Gwamna Ba, Inji Jam’iyyar ADC Ta Kebbi

MASU ALAKA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Labarai

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari
Labarai

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026
Next Post
Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas

Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas

LABARAI MASU NASABA

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.