ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Gabas Ta Tsakiya: Gwamnatin Tarayya Ta Fara Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Iran

by Sadiq
4 months ago
Iran

Gwamnatin Tarayya ta fara kwashe ‘yan Nijeriya da ke zaune a ƙasar Iran waɗanda suka nuna cewa suna son a dawo da su gida.

An fara fitar da su ta kan iyakar Iran zuwa ƙasar Armenia domin tabbatar da tsaron lafiyarsu yayin da rikici ke ci gaba da ƙamari a yankin Gabas ta Tsakiya.

  • Kotu A Norway Ta Ɗaure Ɗan Wasan Nijeriya Kan Zargin Aikata Fyaɗe
  • Saudiyya Ta Rage Samar Da Man Fetur Saboda Matsalar Jigila A Hormuz

Shugabar Hukumar ‘Yan Nijeriya Mazauna Ƙasashen Waje (NiDCOM), Abike Dabiri-Erewa ce, ta bayyana hakan a wani saƙo da ta wallafa a shafinta na X, a ranar Talata.

ADVERTISEMENT

Ta ce kawo yanzu babu wani ɗan Nijeriya da rikicin ya shafa a Iran.

Ta kuma ƙara da cewa jami’an ofishin jakadancin Nijeriya suna kan iyakar Iran da Armenia domin karɓar ‘yan Nijeriya da taimaka musu su tsallaka iyakar zuwa waje mafi aminci.

LABARAI MASU NASABA

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Dangane da dawo da su gida ta jirgin sama, Dabiri-Erewa ta ce a halin yanzu sararin samaniyar yankin ba shi da tsaro.

Duk da haka, ta tabbatar wa ‘yan Nijeriya da ke Gabas ta Tsakiya cewa Gwamnatin Tarayya na shirye-shiryen kwaso su da zarar an samu damar hakan.

Ta ce: “Kwanaki biyu da suka wuce an samu jirgi daga Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa zuwa Legas kafin daga bisani wani hari ya sa aka rufe sararin samaniyar.”

Ta kuma ƙara da cewa: “Da zarar an buɗe sararin samaniyar, tawagar Gwamnatin Tarayya da ta ƙunshi jami’ai daga ma’aikatu daban-daban za su fara aikin kwaso ‘yan Nijeriya zuwa gida.”

Matakin na zuwa ne bayan rikicin da aka fara tun a ranar 28 ga watan Fabrairu, bayan harin da Amurka da Isra’ila suka kai wa Iran.

MASU ALAKA

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Ana Ganin Yanayi Na Tabbas Wajen Tarukan Majalisun Kasar Sin

Ana Ganin Yanayi Na Tabbas Wajen Tarukan Majalisun Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.