Tun bayan ɓarkewar zanga-zangar tsadar rayuwa da ta rikiɗe ta koma tarzomar kin jinin gwamnati daga wasu acikin al’ummar Iran a ƙarshen Disamba 2025 da farkon Janairu 2026, akwai karuwar muhawara tsakanin Iran da Amurka, ciki har da tsauraran kalamai da barazanar juna tsakanin shugabannin kasashen biyu.
Amurka ta nuna goyon baya ga masu zanga-zangar ta Iran, tana kira ga gwamnatin Tehran da ta daina yin amfani da karfi wajen murkushe su, wanda hakan ya sanya Shugaba Donald Trump ya yi barazanar cewa, Washington na iya “taya” masu zanga-zangar ko ma ɗaukar matakai idan hukumomin Iran suka yi amfani da karfi wajen kashe mutane.
- Yanzu- Yanzu An Sako Masu Ibadar da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna
- Ƴansanda 5,000 Za Su Yi Ritaya A 2026
A nata martanin, Iran ta zargi Amurka da tsoma baki sosai a harkokinta na cikin gida, tana cewa wannan wani yunkuri ne na kifar da gwamnatinta, wanda kuma ba za ta lamunci hakan ba. A cikin martanin da aka fitar a hukumance, Tehran ta yi gargaɗin cewa, duk wani yunƙurin Washington na kai hari Tehran zai dagula zaman lafiyar yankin, inda ta sha alwashin mayar da martanin hari kan duk wani sansanin sojin Amurka dake yankin da kuma duk kasar da ta bari Amurka ta yi amfani da kasarta ko sararin samaniyarta wurin kai mata (Iran) hari.
Amurka dai, tuni ta tura jiragen yakinta na ruwa masu ɗaukar jiragen yaki zuwa tekun kusa da Iran, inda ita kuma Iran ta sha alwashin mayar da kakkausar martani.
Tataburzar siyasar da ake yi game da siyasar yankin gabas ta tsakiya na ci gaba da tona asirin yadda turawan yamma ke ci gaba da cin tuwo da miyar bara. Tun daga rikicin yankin Palasdinu zuwa abubuwan da ke faruwa kwanan nan kan batun Iran, duk da a zahiri suna haifar da koma-baya, amma kuma a badini suna kara mayar da burin yammacin duniyar tamkar mafarkin da ba zai taba zama gaskiya ba saboda kiyayyarsu da take karuwa a zukatan al’ummomin yankin.
Bayan harin Amurka da Isra’ila na shekarar 2025 da gajeren rikicin da ya biyo baya, wasu masana sun lura cewa maimakon hakan ya raunana Iran daga zuci, sai ya kara mata kwarin gwiwar karfafa matsayinta na tsaro tare da kara zurfafa dangantakarta ta diflomasiyya musamman da manyan kasashe masu fada-a-ji a yankin Asiya.
Fankamar yammacin duniya ita ce karfin tattalin arziki da kuma makamai. Amma kuma yaki daga zuciya ake cin nasararsa. Ko an zubar da jini, wutar gaba mai ruruwa a zukatan al’umma ba ta mutuwa, sai dai ta sake rincabe nasarar da aka ci. Ga misalai nan a kasashen da Amurka da kawayenta suka afka musu, kamar Afghanistan, Iraqi da Libiya da kuma sauran kasashen da suka yi musu munakisa.
Duk da cewa takunkuman da aka kakabawa Iran sun lalata tattalin arzikinta kuma sun shafi rayuwar talakawan kasar, amma kuma ba su samar da tasirin siyasa da Washington ta yi tsammani ba. A halin yanzu, galibin fushin da al’ummar Iran ke yi bisa yanayin da aka jefa su ciki na kara karkata zuwa ga wadanda suka kakaba takunkuman duk kuwa da zanga-zangar da aka yi kwanan baya, saboda haka, matsin tattalin arzikin yammacin duniya bai ba su asalin muradin abin da suke nema ba.
A wani tsokaci da ya yi ta kafar sada zumunta, wani farfesa daga tsangayar nazarin muhalli ta Jami’ar BUK dake Nijeriya, Malam Aliyu Salisu Barau ya yi nuni da cewa, ya kamata kasashen yammacin duniya su fahimci rashin tasirin dabi’ar tilastawa a wannan zamani, inda ya kafa hujja da cewa, sassauta takunkumi da inganta yanayin jin kai na iya sauya ra’ayoyin al’umma fiye da tayar da husuma. Kazalika, kyakkyawar diflomasiyya da hulda ta tattalin arziki na iya samar da yanayi mafi dacewa na ci gaba da kuma zaman lafiya na dogon lokaci.
Komai za mu ce, sai dai muce, Allah shi kyauta.














Discussion about this post