Rundunar soja ta kasar Sin (PLA) ta ce ta bi jirgin ruwan yaki na De Ruyter na kasar Holland, wanda ya tsallake mashigin tekun Taiwan na kasar Sin a kwanan baya, tare da sanya masa ido.
Kakakin rundunar sojan a yankin gabashin kasar, Xu Chenghua ne ya sanar da hakan a jiya Juma’a, inda ya ce sojojin kasar Sin za su ci gaba da zama kan baka a kokarin kare ikon mulkin kai da tsaron kasar Sin, gami da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin da kasar ke ciki.
Rahotanni na cewa, kafin jirgin ruwan yaki na De Ruyter ya tsallake mashigin tekun Taiwan, ya shiga yankin tekun kasar Sin dake dab da tsibiran Xisha Qundao ta wata haramtacciyar hanya. Ban da haka, wani jirgin sama mai saukar ungulu ya tashi tare da sauka a kan jirgin ruwan sau da dama, matakin da ya zama keta ikon mallakar yankin sararin samaniya na kasar Sin. (Bello Wang)














Discussion about this post