Aƙalla mutum biyar ne suka rasa rayukansu bayan wasu mahara ɗauke da makamai sun kai hari ƙauyen Gwan-Ajang da ke gundumar Foron a ƙaramar hukumar Barkin Ladi ta Jihar Filato a daren ranar Lahadi.
Rundunar ‘yansandan Jihar Filato ta ce harin ya faru ne da misalin karfe 9:30 na dare yayin da mazauna yankin ke gudanar da wani taro.
Kakakin rundunar, Alfred Alabo, ya ce jami’an tsaro sun isa wajen bayan samun kiran gaggawa, amma sun tarar da wasu mutane kwance cikin jini.
‘Yansanda sun tabbatar da mutuwar mutum biyar tare da bayyana cewa an dawo da zaman lafiya a yankin.
Hukumomin tsaro sun ce suna gudanar da sintirin haɗin gwiwa da bincike domin gano tare da cafke waɗanda suka kai harin.
Sai dai wata ƙungiyar matasan Berom ta yi iƙirarin cewa mutum bakwai ne suka mutu, yayin da sama da mutum 10 suka samu munanan raunuka kuma suna karɓar magani a asibiti.
Hukumomin tsaro sun ce bincike na ci gaba da gudana yayin da aka ƙara tsaurara matakan tsaro a yankin domin kamo waɗanda ke da hannu a harin.















Discussion about this post