Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Babachir Lawal, ya yi hasashen cewa Shugaba Bola Tinubu zai lashe zaɓen shugaban ƙasa na 2027 cikin sauƙi.
Lawal ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Channels, jim kaɗan bayan ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar ADC.
Ya ce ya yanke shawarar barin harkokin siyasa ne saboda rashin gamsuwa da yadda ake tafiyar da siyasa a Najeriya.
A cewarsa, yanzu zai mayar da hankali kan harkokin noma da kuma ayyukan addini.
Lawal, wanda ya yi haɗaka da ‘yan adawa ya amince da ADC a matsayin jam’iyyarsa, ya ce Tinubu zai yi wahalar kayarwa a zaɓe mai zuwa.
Ya kuma yi iƙirarin cewa idan maganar yin maguɗi ne ke ƙayyade nasara a zaɓe, babu wani ɗan siyasa da zai iya yin takara da Tinubu.
Haka kuma ya ce tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar zai yi wahala ya yi takara da Tinubu a zaɓen 2027.
Tsohon sakataren ya kuma bayyana cewa ba zai goyi bayan Peter Obi ba a zaɓen 2027, yana mai cewa ya daina harkar siyasa gaba ɗaya.
“Ba zan goyi bayan Peter Obi ba. Ba na son shiga komai,” in ji Lawal.















Discussion about this post