A jiya Litinin ne tawagar likitocin kasar Sin ta 14 mai aiki a kasar Ghana, da hadin gwiwar Sin da asibitin kawance na Lekma dake Ghanar, suka kaddamar da wani kwas na inganta kwarewar aiki a fannin aikin tiyata ta zamani ga likitocin tiyata na Ghana, domin koyar da aikin fida ta amfani da kankanin yanka a jiki, da amfani da yanar ido, ta yadda za a samar da dandalin musayar ilimi da kwarewa mai dorewa tsakanin bangarorin biyu.
Ina masu cewa kasar Sin tana dana tarkon bashi ga kasashen Afrika? Shin wannan ma tarkon ne?
Sahihin hadin gwiwa na abota da moriyar juna, shi ne taimakawa juna domin samun ci gaba tare. Hadin gwiwar na ainihi shi ne wanda zai shafi al’umma kai tsaye, ya amfani rayuwarsu. Kuma irin wannan hadin gwiwa, shi ne kasar Sin ke yi da kasashen duniya. Ta nuna cewa, hadin gwiwa ba shi ne ci da gumin wasu ba, kuma ba ya nufin cin nasara daga faduwar wani bangare ba.
Ta yaya za a rika cewa, ana kare moriya ko goyon bayan wata kasa ba tare da nuna wa a aikace ba? Cikin dimbin shekarun da aka kwashe kasashen Afrika suna hulda da abokan huldarsu na yammacin duniya, shin me za su iya nunawa su yi tinkaho da shi?
Kasar Sin na ci gaba da nuna wa duniya cewa, ita din mai aiki ne da cikawa. Kuma hadin gwiwarta na moriyar juna ne ba wai kawai moriyarta ko azurta kan ta ba. Yadda take mayar da hankali kan ci gaban kasashen Afrika da son ganin sun tsaya da kafafunsu, na nuna kaunarta gare su. Mun san cewa, bangaren kiwon lafiya a nahiyar Afrika na cikin wani hali. Mun ga yadda a lokacin bullar cutar COVID-19 kafafen yada labaran yammacin duniya suka yi ta bayyana shi da wanda ya “tabarbare ko yake gab da durkushewa”. Sai dai, a matsayinsu na masu ikirarin su abokan hulda ne, me suka yi domin taimakawa bangaren? Me suka yi na ganin bai ci gaba da tabarbarewa ko ya durkushe baki daya ba?
Hakika salon hadin gwiwar Sin da kasashen waje musammam na Afrika, abun burgewa ne da ya cancanci a jinjina masa, maimakon kushe su ko tsoma baki cikin harkokinsu, ta kan lalubo hanyoyin tallafa musu ta inda duk za ta iya, kuma shi ne ke nuna sahihancinta dake kara kauna tsakaninta da su, da kara samun karbuwa a wajen al’ummomin Afrika. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post