Sanata Aliyu Wamakko, mai wakiltar Sakkwato ta Arewa a Majalisar Dattawa, ya yi Allah-wadai da ƙaruwar hare-haren ‘yan bindiga, da masu garkuwa da mutane da sauran ayyukan ta’addanci da ke haddasa asarar rayuka da dukiyoyi a sassan Nijeriya.
A wata sanarwa da ofishinsa ya fitar, tsohon gwamnan jihar Sakkwato ya buƙaci gwamnatin tarayya da ta ɗauki matakan gaggawa domin ƙarfafa tsaro a faɗin ƙasar, tare da tabbatar da cewa jama’a na rayuwa cikin kwanciyar hankali ba tare da fargaba ba.
Wamakko ya ce yawaitar hare-haren da ake gani a baya-bayan nan na buƙatar haɗin gwuiwar gwamnati, da hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki domin daƙile matsalar kafin ta ƙara ƙamari.
Ya jaddada cewa kare rayuka da dukiyoyin al’umma shi ne babban nauyin da ke kan gwamnati, yana mai cewa ba za a ci gaba da kallon yadda ‘yan ƙasa ke rasa rayukansu a hannun masu aikata laifuka ba tare da ɗaukar ƙwararan matakai ba.















Discussion about this post