ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar NDLEA Ta Lalata Sama Da Tan 12 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano

by Sani Anwar
3 weeks ago
Kano

Hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta ƙasa (NDLEA) ta Jihar Kano, ta bankaɗo wasu miyagun ƙwayoyi da suka kai kimanin kilo 12,233.946 (kimanin tan 12.2), na haramtattun ƙwayoyi da abubuwan da aka kama ta hanyar gudanar da ayyukan sirri a faɗin Jihar Kano da kuma filin jirgin saman Malam Aminu Kano.

Atisayen, wanda kwamandan rundunar ta Kano, CN Dahiru Yahaya Lawal ya jagoranta, wani ɓangare ne na yaƙin wanda hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi (WADA) ke yi da nufin daƙilewa da gurfanar da su da kuma kawar da miyagun ƙwayoyi na din-din-din.

Baje kolin lalatawar ya haɗa da kilo 11,890.427 da rundunar ta kama da kuma 343.519 da aka kama a filin jirgin saman Malam Aminu Kano.

ADVERTISEMENT

Magungunan sun haɗa da ‘cannabis satiɓa, tramadol, codeine, heroin, hodar iblis, methamphetamine, pregabalin, diazepam, pentazocine da sauran makamantansu.

A cewar hukumar ta NDLEA, an kama waɗanda aka kaman ne daga wani samame da jami’an leƙen asiri suka jagoranta da hare-hare na musamman da suka haɗa da ‘Operation Sharar Mafaka da Operation Ramadan Mubarak’.

LABARAI MASU NASABA

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Binciken ya kuma gano wasu kayayakin maɓoyar muggan ƙwayoyi da suka haɗa da ramuka da kogo a yankin Rimin Kebe, wanda ya nuna hanyoyin da masu fataucin ke bi wajen gujewa jami’an tsaro.

Kwamanda Lawal ya bayyana cewa, tun daga watan Janairun 2026, rundunar ta kama mutane 904 da ake zargi, maza 869 da mata kuma 35, sannan sun kama fiye da tan 2.5 na haramtattun abubuwa tare da samun sama da hukunce-hukunce 54.

Wasu da aka samu da laifin, ya ce; an yanke musu hukuncin ɗaurin shekara 15 a gidan yari.

Ya jaddada cewa, duk da cewa; aiwatar da doka na da matuƙar muhimmanci, yaƙi da shaye-shayen miyagun ƙwayoyi na buƙatar ɗaukar matakin haɗin gwiwa da ya haɗa da hukumomin tsaro, shugabannin gargajiya da na addini, cibiyoyin ilimi, masu ɗaukar ma’aikata, iyaye da kuma al’umma.

Lawal ya yaba wa Shugaba kuma Babban Jami’in Hukumar NDLEA, Brig.-Gen. Mohamed Buba Marwa (Rtd), CON, OFR, bisa jagorancinsa, ya kuma yaba wa gwamnatin Jihar Kano, ƙarƙashin Gwamna Abba Kabir Yusuf, bisa ci gaba da bayar da goyon baya, musamman a aikin yaƙi da zaizayar ƙasa a Rimin Kebe, wanda ya kawar da maɓoyar masu laifi.

Ya kuma yaba wa alƙalan babbar kotun tarayya, bisa hukuncin da suka yanke a kan lokaci tare da jinjina wa daraktan ayyuka da bincike na ƙasa, DCGN Ahmad Sulaiman Ningi, bisa sadaukarwar da ya yi.

Kano
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

MASU ALAKA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Labarai

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci
Rahotonni

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Next Post
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

LABARAI MASU NASABA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.