Hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta ƙasa (NDLEA) ta Jihar Kano, ta bankaɗo wasu miyagun ƙwayoyi da suka kai kimanin kilo 12,233.946 (kimanin tan 12.2), na haramtattun ƙwayoyi da abubuwan da aka kama ta hanyar gudanar da ayyukan sirri a faɗin Jihar Kano da kuma filin jirgin saman Malam Aminu Kano.
Atisayen, wanda kwamandan rundunar ta Kano, CN Dahiru Yahaya Lawal ya jagoranta, wani ɓangare ne na yaƙin wanda hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi (WADA) ke yi da nufin daƙilewa da gurfanar da su da kuma kawar da miyagun ƙwayoyi na din-din-din.
Baje kolin lalatawar ya haɗa da kilo 11,890.427 da rundunar ta kama da kuma 343.519 da aka kama a filin jirgin saman Malam Aminu Kano.
Magungunan sun haɗa da ‘cannabis satiɓa, tramadol, codeine, heroin, hodar iblis, methamphetamine, pregabalin, diazepam, pentazocine da sauran makamantansu.
A cewar hukumar ta NDLEA, an kama waɗanda aka kaman ne daga wani samame da jami’an leƙen asiri suka jagoranta da hare-hare na musamman da suka haɗa da ‘Operation Sharar Mafaka da Operation Ramadan Mubarak’.
Binciken ya kuma gano wasu kayayakin maɓoyar muggan ƙwayoyi da suka haɗa da ramuka da kogo a yankin Rimin Kebe, wanda ya nuna hanyoyin da masu fataucin ke bi wajen gujewa jami’an tsaro.
Kwamanda Lawal ya bayyana cewa, tun daga watan Janairun 2026, rundunar ta kama mutane 904 da ake zargi, maza 869 da mata kuma 35, sannan sun kama fiye da tan 2.5 na haramtattun abubuwa tare da samun sama da hukunce-hukunce 54.
Wasu da aka samu da laifin, ya ce; an yanke musu hukuncin ɗaurin shekara 15 a gidan yari.
Ya jaddada cewa, duk da cewa; aiwatar da doka na da matuƙar muhimmanci, yaƙi da shaye-shayen miyagun ƙwayoyi na buƙatar ɗaukar matakin haɗin gwiwa da ya haɗa da hukumomin tsaro, shugabannin gargajiya da na addini, cibiyoyin ilimi, masu ɗaukar ma’aikata, iyaye da kuma al’umma.
Lawal ya yaba wa Shugaba kuma Babban Jami’in Hukumar NDLEA, Brig.-Gen. Mohamed Buba Marwa (Rtd), CON, OFR, bisa jagorancinsa, ya kuma yaba wa gwamnatin Jihar Kano, ƙarƙashin Gwamna Abba Kabir Yusuf, bisa ci gaba da bayar da goyon baya, musamman a aikin yaƙi da zaizayar ƙasa a Rimin Kebe, wanda ya kawar da maɓoyar masu laifi.
Ya kuma yaba wa alƙalan babbar kotun tarayya, bisa hukuncin da suka yanke a kan lokaci tare da jinjina wa daraktan ayyuka da bincike na ƙasa, DCGN Ahmad Sulaiman Ningi, bisa sadaukarwar da ya yi.














