ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar NDLEA Ta Lalata Sama Da Tan 12 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano

by Sani Anwar
1 day ago
Kano

Hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta ƙasa (NDLEA) ta Jihar Kano, ta bankaɗo wasu miyagun ƙwayoyi da suka kai kimanin kilo 12,233.946 (kimanin tan 12.2), na haramtattun ƙwayoyi da abubuwan da aka kama ta hanyar gudanar da ayyukan sirri a faɗin Jihar Kano da kuma filin jirgin saman Malam Aminu Kano.

Atisayen, wanda kwamandan rundunar ta Kano, CN Dahiru Yahaya Lawal ya jagoranta, wani ɓangare ne na yaƙin wanda hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi (WADA) ke yi da nufin daƙilewa da gurfanar da su da kuma kawar da miyagun ƙwayoyi na din-din-din.

Baje kolin lalatawar ya haɗa da kilo 11,890.427 da rundunar ta kama da kuma 343.519 da aka kama a filin jirgin saman Malam Aminu Kano.

ADVERTISEMENT

Magungunan sun haɗa da ‘cannabis satiɓa, tramadol, codeine, heroin, hodar iblis, methamphetamine, pregabalin, diazepam, pentazocine da sauran makamantansu.

A cewar hukumar ta NDLEA, an kama waɗanda aka kaman ne daga wani samame da jami’an leƙen asiri suka jagoranta da hare-hare na musamman da suka haɗa da ‘Operation Sharar Mafaka da Operation Ramadan Mubarak’.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Binciken ya kuma gano wasu kayayakin maɓoyar muggan ƙwayoyi da suka haɗa da ramuka da kogo a yankin Rimin Kebe, wanda ya nuna hanyoyin da masu fataucin ke bi wajen gujewa jami’an tsaro.

Kwamanda Lawal ya bayyana cewa, tun daga watan Janairun 2026, rundunar ta kama mutane 904 da ake zargi, maza 869 da mata kuma 35, sannan sun kama fiye da tan 2.5 na haramtattun abubuwa tare da samun sama da hukunce-hukunce 54.

Wasu da aka samu da laifin, ya ce; an yanke musu hukuncin ɗaurin shekara 15 a gidan yari.

Ya jaddada cewa, duk da cewa; aiwatar da doka na da matuƙar muhimmanci, yaƙi da shaye-shayen miyagun ƙwayoyi na buƙatar ɗaukar matakin haɗin gwiwa da ya haɗa da hukumomin tsaro, shugabannin gargajiya da na addini, cibiyoyin ilimi, masu ɗaukar ma’aikata, iyaye da kuma al’umma.

Lawal ya yaba wa Shugaba kuma Babban Jami’in Hukumar NDLEA, Brig.-Gen. Mohamed Buba Marwa (Rtd), CON, OFR, bisa jagorancinsa, ya kuma yaba wa gwamnatin Jihar Kano, ƙarƙashin Gwamna Abba Kabir Yusuf, bisa ci gaba da bayar da goyon baya, musamman a aikin yaƙi da zaizayar ƙasa a Rimin Kebe, wanda ya kawar da maɓoyar masu laifi.

Ya kuma yaba wa alƙalan babbar kotun tarayya, bisa hukuncin da suka yanke a kan lokaci tare da jinjina wa daraktan ayyuka da bincike na ƙasa, DCGN Ahmad Sulaiman Ningi, bisa sadaukarwar da ya yi.

Kano
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnati Ta Amince Da Inganta Cibiyar Kula Da Saran Maciji A Gwambe
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

MASU ALAKA

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
Labarai

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi
Labarai

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Next Post
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.