ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar GDI Na Ci Gaba Da Samun Karbuwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 month ago
GDI

A matsayin babbar kasa a duniya, Sin na ci gaba da samun kwarewa a fannin ikonta da kuma kwazon gina kanta, kana da samar da gudunmawa ga ci gaban duniya baki daya. Bisa hakan ne ma ta gabatarwa duniya shawarar bunkasa ci gaban duniya ko GDI a takaice, wadda manufarta ita ce taimakawa sassa kasa da kasa da dabarun cimma burikansu, da cimma nasarar ajandar MDD ta wanzar da ci gaban duniya.

Kazalika, shawarar ta zo a gabar da duniya ke fama da gibin ci gaba wanda ke kara fadada a zahiri.Tun bayan da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarar a shekarar 2021, Sin ta mayar da hankali ga yayata alfanunta, da nufin baiwa dukkanin kasashen duniya, musamman ma masu tasowa damar amfana daga damarmakin ci gaba.

Kuma jim kadan da kaddamar da ita, shawarar GDI ta samu matukar karbuwa daga MDD, da hukumomin kasa da kasa da ma akasarin kasashen duniya, duba da yadda ta fayyace dabarun warware batutuwan gaggawa na al’ummun duniya, irinsu zaman lafiyar duniya, da ci gaba da kuma hadin gwiwa.Ko shakka babu, sassan kasa da kasa suna fuskantar manyan kalubale ta fuskar aiwatar da ajandar wanzar da ci gaba ta MDD ta nan zuwa shekarar 2030, yayin da gibin ci gaban duniya ke kara fadada. Har ila yau, batutuwan ci gaban duniya ba sa samun kulawar da ta kamata.

ADVERTISEMENT

Wasu kasashen duniya na daukar matsaya ta kashin kai, da baiwa kasuwa kariya, kana wasu na kafa shingaye, da kokarin mayar da wasu saniyar-ware, matakan da ke gurgunta tsarin samarwa da rarraba hajojin masana’antun kasa da kasa. Dukkanin wadannan dalilai da ma wasu, suna taka rawa wajen fadada kalubalen siyasar yankuna da duniya ke fama da su, suna kara ta’azzara sauyin yanayi, da matsalar makamashi da ta kamfar abinci, tare da illata moriyar kasashen duniya baki daya, musamman ma kasashe masu tasowa, tare da mayar da hannun agogo baya game da burin cimma nasarar ajandar ci gaba mai dorewa ta MDD ta nan zuwa shekarar 2030.

To sai dai kuma, bisa kwarewar da ta samu a tsawon shekaru, musamman ta fuskar gwada dabarun samar da ci gaba, da ayyukan yaki da fatara a yankunan karkara, da sauran manufofi na mayar da al’umma gaban komai, kasar Sin ta baiwa duniya gudunmawar shawarar GDI. Kuma yayin da ake cika kusan shekaru biyar da gabatar da ita, shawarar na samun manyan nasarori daga matakin gabatarwa zuwa na aiwatarwa.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

A yanzu haka, tana samun karin goyon baya, inda karin kasashe sama da 130 suka shiga cikinta, baya ga hukumomin kasa da kasa masu yawa, kana ya zuwa yanzu, sama da kasashe 80 suka shiga rukunin abota na wannan shawara ta GDI, matakin da ke tabbatar da kabuwarta da kuma alfanunta ga duniya. (Saminu Alhassan)

GDI
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
GDI
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
JKS Ta Shirya Taron Karawa Juna Sani Da Nufin Sauraron Shawarwari Dangane Da Aikin Raya Tattalin Arziki

JKS Ta Shirya Taron Karawa Juna Sani Da Nufin Sauraron Shawarwari Dangane Da Aikin Raya Tattalin Arziki

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.