ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Riba Ce Ga Kasashe Masu Tasowa

by CMG Hausa
4 years ago
Ziri daya

Yayin da kasashen duniya ke ci gaba da nazari, da fafutukar neman kyakkyawar makoma a wannan mawuyacin lokaci da duniya take ciki, musamman ta fuskar koma bayan tattalin arziki, da gurguncewar sassa daban daban na ci gaba, sakamakon bullar annobar COVID-19, da rikicin kasar Ukraine da suka haifar da mummunar illa ga duniya, a hannu guda, kasashe musamman masu tasowa, na da kyakkyawan fatan samun ci gaba da wadata, karkashin ayyukan da ake ci gaba da gudanarwa, bisa shawarar nan ta Ziri Daya da Hanya Daya wadda kasar Sin ta gabatarwa duniya.

Cikin irin wadannan ayyuka da a yanzu haka ke daf da kammala, akwai ginin tashar teku mai zurfi ta yankin Lekki na jihar Lagos dake kudu maso yammacin Najeriya, wadda kasar Sin ta tallafa wajen gudanarwa.

  • An Shirya Tattaunawar Tiangong Tsakanin ‘Yan Sama Jannatin Sin Da Matasan Afirka Cikin Nasara

’Yan Najeriya da dama, da masana tattalin arziki a kasar, na jinjinawa kasar Sin, bisa aiwatar da wannan muhimmin aiki mai tarin alfanu, wanda zai fadada damar Najeriya ta karbar manyan jiragen dakon kayayyaki daga sassan duniya daban daban.

ADVERTISEMENT

Aikin wanda zai lashe tsabar kudi har dalar Amurka biliyan 1.5, a yanzu ya kai kaso 95 bisa dari na kammala, ana kuma sa ran gama shi baki daya zuwa karshen shekarar nan ta 2022. Tashar za ta hade da yankin ciniki cikin ’yanci na jihar ta Lagos.

Da zarar tashar ta kammala, za ta zamo ta 3 da Najeriya ke da su, baya ga tsoffin tashoshin ruwa masu karbar jiragen ruwa guda biyu dake fama da cinkoso.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Sabanin tsofannin tashoshin biyu, sabuwar tashar teku mai zurfi ta Lekki, za ta iya karbar kayan da yawansu zai kai na sama da manyan sundukan dakon kaya masu fadin kafa 20 har miliyan 2.7 a duk shekara, kana tashar tekun mai zurfi, za ta samarwa Najeriya zarafin karbar sundukan dakon kayayyaki daga 3,000 zuwa 20,000 a kullum, wanda hakan ya sanya tashar zama daya daga ayyuka mafi muhimmanci da Najeriya za ta ci gajiyar su, karkashin shawarar Ziri Daya da hanya Daya.

Ko shakka babu wannan muhimmin aiki ne da zai bunkasa tattalin arzikin Najeriya ta fuskar samun karin haraji, da guraben ayyukan yi, da fadada damammaki na kasuwanci da cinikayya, baya ga rage tsadar kudaden fito, da kara zamanintar da salon ba da hidimomin shige da fice da tashar za ta yi a kasa irin Najeriya, wadda ita ce mafi girman tattalin arziki a nahiyar Afirka. (Saminu Hassan)

Ziri daya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
PDP Ta Koka Kan Yadda Jami’an CJTF Ke Cin Zarafin ‘Ya’Yanta A Borno

PDP Ta Koka Kan Yadda Jami'an CJTF Ke Cin Zarafin 'Ya'Yanta A Borno

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.