ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Riba Ce Ga Kasashe Masu Tasowa

by CMG Hausa
4 years ago
Ziri daya

Yayin da kasashen duniya ke ci gaba da nazari, da fafutukar neman kyakkyawar makoma a wannan mawuyacin lokaci da duniya take ciki, musamman ta fuskar koma bayan tattalin arziki, da gurguncewar sassa daban daban na ci gaba, sakamakon bullar annobar COVID-19, da rikicin kasar Ukraine da suka haifar da mummunar illa ga duniya, a hannu guda, kasashe musamman masu tasowa, na da kyakkyawan fatan samun ci gaba da wadata, karkashin ayyukan da ake ci gaba da gudanarwa, bisa shawarar nan ta Ziri Daya da Hanya Daya wadda kasar Sin ta gabatarwa duniya.

Cikin irin wadannan ayyuka da a yanzu haka ke daf da kammala, akwai ginin tashar teku mai zurfi ta yankin Lekki na jihar Lagos dake kudu maso yammacin Najeriya, wadda kasar Sin ta tallafa wajen gudanarwa.

  • An Shirya Tattaunawar Tiangong Tsakanin ‘Yan Sama Jannatin Sin Da Matasan Afirka Cikin Nasara

’Yan Najeriya da dama, da masana tattalin arziki a kasar, na jinjinawa kasar Sin, bisa aiwatar da wannan muhimmin aiki mai tarin alfanu, wanda zai fadada damar Najeriya ta karbar manyan jiragen dakon kayayyaki daga sassan duniya daban daban.

ADVERTISEMENT

Aikin wanda zai lashe tsabar kudi har dalar Amurka biliyan 1.5, a yanzu ya kai kaso 95 bisa dari na kammala, ana kuma sa ran gama shi baki daya zuwa karshen shekarar nan ta 2022. Tashar za ta hade da yankin ciniki cikin ’yanci na jihar ta Lagos.

Da zarar tashar ta kammala, za ta zamo ta 3 da Najeriya ke da su, baya ga tsoffin tashoshin ruwa masu karbar jiragen ruwa guda biyu dake fama da cinkoso.

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Sabanin tsofannin tashoshin biyu, sabuwar tashar teku mai zurfi ta Lekki, za ta iya karbar kayan da yawansu zai kai na sama da manyan sundukan dakon kaya masu fadin kafa 20 har miliyan 2.7 a duk shekara, kana tashar tekun mai zurfi, za ta samarwa Najeriya zarafin karbar sundukan dakon kayayyaki daga 3,000 zuwa 20,000 a kullum, wanda hakan ya sanya tashar zama daya daga ayyuka mafi muhimmanci da Najeriya za ta ci gajiyar su, karkashin shawarar Ziri Daya da hanya Daya.

Ko shakka babu wannan muhimmin aiki ne da zai bunkasa tattalin arzikin Najeriya ta fuskar samun karin haraji, da guraben ayyukan yi, da fadada damammaki na kasuwanci da cinikayya, baya ga rage tsadar kudaden fito, da kara zamanintar da salon ba da hidimomin shige da fice da tashar za ta yi a kasa irin Najeriya, wadda ita ce mafi girman tattalin arziki a nahiyar Afirka. (Saminu Hassan)

Ziri daya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
Daga Birnin Sin

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
Next Post
PDP Ta Koka Kan Yadda Jami’an CJTF Ke Cin Zarafin ‘Ya’Yanta A Borno

PDP Ta Koka Kan Yadda Jami'an CJTF Ke Cin Zarafin 'Ya'Yanta A Borno

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.