ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shehu Ibrahim Inyass: Gwarzon Musulunci A Karne Na 20 (II)

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
3 years ago
shehu ibrahim inyass

Shehu Ibrahim (RA) ya taimaki addini da kayan zamaninsa da ya tarar wanda Turawan mulkin mallaka suka yi amfani da su. Shi ne farkon Musulmin da ya yi haka. Ya yi amfani da Rediyo, da Tarho, da Rikoda, da Kamara wajen isar da sakon Musulunci. Don har yau, akwai gidahumin musulmin da yake ganin yin hoto kafirci ne, amma Shehu Ibrahim ne ya wayar mana da kai a kan amfani da wadannan kayan a cikin addininmu na Musulunci. Haka nan amfani da motoci da jirgin sama, da lasifika, da agogo, da zuwa asibitoci.

Shehu Ibrahim yana daga cikin wadanda ya tilasta wa almajiransa zuwa asibiti wanda a da ba a yarda da hakan ba. Sannan ya koyar da yin karatu irin wannan da ake yi na zamani a makarantu.

  • Ganin Girma Da Kwarjinin Annabi (SAW)

Shehu Ibrahim (RA) shi ne farkon Musulmi kuma Malami da ya waye ya san cewa “technology” ba kishiyar addini ba ne. Shi ne farkon malamin da ya yarda cewa Turawa sun je duniyar wata a shekarar 1969 (combo apolo 11) har ma ya yi littafi a kan wannan. Kuma ya yi wa shugaban Amurka na lokacin wasika a kan wannan (documents suna nan a kan haka). Su Malaman Saudiyya cewa suka yi ma duk wanda ya yarda cewa an je duniyar watan kafiri ne, su kuma na Azahar (Misra) suka ce sam ma ba zai yiwu ba.

ADVERTISEMENT

Amma Shehu Ibrahim ne ya gamsar da su (da hujja) har suka yarda da abin.
Shehu Ibrahim (RA) ya kewaya kasashen duniya har Chana, Beijin, Honkon, da sauran sassan karshen Asiya don taimakon Musulunci. Ya hada kan Musulmi Larabawa da Bakar Fata. Yana da kishi na hakika a kan addininsa na Musulunci mai tsafta ba na ta’addanci ba.

Shehu Ibrahim (RA) yana da kishi a kan Afirka. Ya yi tsayuwar daka tare da ba da gudummawa ga samun ‘yancin duk wata kasa ta Afirka ciki har da kasarmu Nijeriya. Yana da kishin mutane bakar fata ‘yan’uwansa.

LABARAI MASU NASABA

Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha

Falalar Neman Tsari Daga Sharrin Shaidan

Bayan haka, Shehu Ibrahim (RA) ne gwarzon namijin da ya tsaya shi kadai ya kori Isra’ila daga kasarsa Senigal wanda nan ne hanyar shigowa Afirka. A lokacin, Faransa ta yiwa Yahudawa izinin shiga Afirka ta Senigal ba tare da takardar biza ba ma. Ba domin Shehu Ibrahim ya kore su ba da mu ma yanzu abin da yake samun Palasdinawa ya same mu. Jamilu Arif, wani danjarida na kasar Misra ya fadi wannan.”

Da yake duniya ta bunkasa da kakkafa kungiyoyi don cimma abubuwa da dama da aka tasa a gaba, Sayyid Isma’il Maidiwani ya yi bayanin cewa Shehu Ibrahim ya ba da gudummawa ta wannan fuskar don ci gaban Musulunci.

Shehu (RA) ya ba da gagarumar gudummawa wajen kafa Rabida ta Malaman Musulunci na Duniya (duk akwai hujjoji a kai a hannu). Sannan ya kafa hadin kan Afirka wanda ta hannunsa ne shugabannin Afirka suka karbi wannan. Ya kuma kafa kungiyoyin da za su taimaki addini irin su Ansarid Dini tare da umurtar almajiransa su kafa, mu nan a Nijeriya akwai Fityanul Islam.

Manyan ‘yanjarida na duniya Turawa da Larabawa da sauran su duk sun yi magana a kan Shehu Ibrahim (RA). Ustazu Abdulkareemin Niyazi ya yi magana a kan Shehu da irin kokarinsa a Jaridar Saudiyya. Haka nan Jamilu Arif na Misra ya yi magana a kan Shehu. Sannan babban malamin Saudiyya Sheikh Muhammad Mahmud Sauwaf a cikin littafin da ya yi mai suna “Yawona Zuwa Kasashen Musulunci” ya yi magana a kan Shehu (RA).

Shehu Ibrahim ne malami bakar fata da ya samu daukakar yiwa Musulmi Sallar Jumma’a a Jami’ar Az’har ta Misra a 1961, wanda kafin shi ba a taba yin wannan ba (RA).

Haka nan ya rike mukamai da yawa a duniya. Shehu ne na Musulunci wanda yake da fahimtoci a cikin Tauhidi, ya warware abubuwan da ya gagari malamai a cikin Tauhidi cikin sauki. Daga cikin mukaman da ya rike a duniya akwai shugaban hadin kan Jami’ar Kairawani da Jami’ar Az’har. Sannan ya rike mataimakin taron Musulunci da aka yi a Karachi ta Pakistan. Yana daga cikin kwamitin da ya kafa Rabida ta Malaman Musulunci na duniya a Makka. Sannan yana cikin kwamitin da ya hada kan jami’o’in Musulunci na duniya a Ribad na Moroko.

Haka nan yana daga cikin babban kwamitin malamai masu yiwa abubuwa hukunci a Musulunci na Misra. Ya rike babban matsayi a taron shekara-shekara na bincike a cikin Musulunci a Misra. Har ila yau, yana da matsayi babba a Majalisar Musulunci ta Jaza’ir da sauran su da dama.

Shehu Ibrahim (RA) ya ci nasara wajen yin kira zuwa shiga addinin Musulunci da hikima da wa’azi mai kyau da jayayya mafi kyau. Idan muka ce Musulunci ma’ana ya hada da Musuluncin, da Imani da Ihsani kamar yadda Hadisin Annabi (SAW) ya fada a Hadisin Jibrilu.

Ba a dinga daukar bangaren Fikhun addini kadai a bar sauran ba kamar yadda ta ke faruwa a wannan zamanin, sai mutum ya hada duk gaba daya.

Amma idan mutum ba zai iya hadawa ba, ya tsaya wa Fikhun addini na makamul Islam din kawai amma kuma ya san cewa akwai karatun Imani na ilmud Tauhidi ba adadi a gabansa da bai sani ba, ballantana kuma ilmut Tasawwuf na Ihsani.

Babban makaminsa na wannan aikin shi ne tsoron Allah, da ilmi sannan ya fahimci zamaninsa (wannan nukuda ce babba). A takaice dai kowa ya tabbatar ba a taba yin Gwarzon Namiji a Musulunci ba irin Shehu Ibrahim (RA) a karne na 20, ba mu Afirka ba har da kasashen Larabawa. Ya bunkasa ilmin addini da Luggar Larabci a Afirka wanda duk ga ‘yan jami’a nan suna ta amfani da karatuttukansa. Bayan wannan, ya watsa ‘ya’ya da jikokinsa da almajiransa a kasashen Turai suna musuluntar da su tare da karantar da su. Tun komawarsa ga Allah har yau; har abada duk wani abu mai amfani za ka ga imma dai ‘ya’yansa ko jikoki ko almajiransa ne suke jagoranci a kai.

Shehu ya kafa alheri, ya yada alherin amma sai aka zo da kishiyarsa, zuwa da kishiyoyinshi abubuwan da ya kafa ne ya kai Afirka cikin bala’in da ake ciki. Amma yanzu da yake an ce ana so a gyara, to lallai a dawo da wannan alheri da kwarewa da cin nasarar da Shehu ya yi, idan aka yi haka da albarkar Annabi (SAW) sai a samu nasarar da ake bukata.

Rikicin wadanda ba su fahimci Shehu Ibrahim Inyass ba kawai ya ta’allaka ne a kan kin tsayawa a matakin ilimin da suke da shi, inda suke kutsawa cikin fannoni ko matakan addini da ba su san komai a kai ba, “suna matakin Fikhun Musulunci amma sai su rika tsallakawa Matakin Imani na Tauhidi ko Ihsani na Sufanci su rika cewa “ya fadi kaza a wuri kaza” alhali ba su da ilmi a kai kwarai da gaske.

Da kowa zai yi adalci ya tsaya a fanninsa sannan ya dauki karatun da Shehu Ibrahim ya yi a kan wannan fannin, da ya san Shehu Shehinsa ne don ya karantar da shi a fannin nasa ma. Haka nan Shehu Ibrahim ya kawar mana da kabilanci a tsakaninmu tare da yaukaka zumunci na ‘yan’uwantaka wanda hatta makiyinsa ma ya yi ma sa shaida a kan wannan. Ko a kan haka, ya dace kwarai da gaske mu rika yin Mauludin Shehu Ibrahim (RA).

shehu ibrahim inyass
Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
+ postsBio
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Falalar Neman Tsari Daga Sharrin Shaidan
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Bukatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

MASU ALAKA

Manzon Allah
Dausayin Musulunci

Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha

June 19, 2026
Falalar Neman Tsari Daga Sharrin Shaidan
Dausayin Musulunci

Falalar Neman Tsari Daga Sharrin Shaidan

June 12, 2026
Bukatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
Dausayin Musulunci

Bukatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

June 5, 2026
Next Post
Bayani A Kan Starlink, Da Yadda Tsarinsa Ya Ke (Kimiyya)

Bayani A Kan Starlink, Da Yadda Tsarinsa Ya Ke (Kimiyya)

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Safarar Kuɗi Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Safarar Kuɗi Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.