• Leadership Hausa
Monday, March 27, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Samar Da Gidajen Yari Na Zamani Masu Cikakken Tsaro

by Yusuf Shuaibu
2 months ago
in Labarai
0
Shirin Samar Da Gidajen Yari Na Zamani Masu Cikakken Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya a karkashin jagorancin Shugaba Muhammadu Buhari, ta dauki matakin kawo karshen yadda ake samun fasa gidajen yari a sassan kasar nan, inda daurarru kan gudu. Fasa gidan yari na baya-bayan nan shi ne wanda ya faru a watan Satumba 2022 a Kuje, Abuja, inda daurarru ciki har da rikakkun masu manyan laifuka suka tsere bayan da ‘yan bindiga suka kai farmaki gidan yarin.

A martaninsa, shugaban kasa ya gaggauta amincewa da a samar gidajen yari na zamani masu dauke da cikakken tsaro guda shida a sassan jihohin kasar nan, ciki har da wanda ake ginawa a garrin Karshi da ke a kan iyakar Jihar Nasarawa da yankin babbar birnin tarayya Abuja wanda ake sa ran zai iya daukar akalla mutum 3,000 a lokaci daya.

  • Hukumar Gidan Yarin Kuje Ta Tabbatar Da Mutuwar Fursuna A Gidan Yarin Kuje

Sabon gidan yarin da za a gina da sauran da za a gina a wasu sassan Nijeriya an shirya samar da kudaden ginawa ne ta wasu kudade daga asusu na musamman da Shugaba Buhari ya amince da su, hakan kuma na daga cikin shirin gwamnatin tarayya na sake fasalin gidajen yarin ta yadda za su yi daidai da zamani, ana son su tashi daga yadda aka san su a da na wajen gallaza wa mutane zuwa gidan gyaran hali.

Sabon gidan yarin da ake ginawa a garin Karshi zai iya daukar mutum 3,000 maza da mata zai kuma samar wa da ma’aikatan hukumar gidajen yari ofishoshin gudanar da ayyukansu ba tare da wata matsala ba.
Shirin da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tsayu don samar da kudaden yi, ana kuma sa ran kammalawa a cikin watan Mayu na wanannan shekarar, ana kuma sa ran shugaba Buhari ne da kansa zai jagoranci bikin kaddamarwa kafin wa’adin mulkinsa ya kare a 29 ga Mayun wannan shekarar.

Samar da sabon gidan yarin na daya daga cikin matakai masu muhimmanci da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya dauka don sake fasalin gidajen yarin kasar nan wanda hakan ya sa tun da farko aka sanya mashi suna daga Gidaje Yarin Nijeriya zuwa Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

Amma wani abin dubawa anan shi ne inda aka shirya gina daya daga cikin gidajen yarin, wato garin Karshi.

Rahottanin sun nuna cewa, akwai wajen fasa duwatsu a tsakiyar inda ake gina gidan yarin, a kan haka ne nuna damuwa a kan abin da fashe-fashen da za a rinka yi zai iya haifarwa ga irin wannan gidan na ajiye manya da kananann masu laifi ga abin da zai iya haifarwa ga lamarin da ya shafi tsaro da jami’an tsaron gaba daya. Wani kamfanin fasa dutse sun bayyana cewa, wajen nasu ne da suka mallaka ta hanu ma’aikatar albarkatun kasa, kuma sun mallaki filin ne da izinin gwamnatin tarayya, kuma suna aiki ne kamar yadda doka ta tanadar.

Tun da farko, Hukumar Babbar Birinin Tarayya ta musammaya musu da wani filin ga Hukumar gidaje amma sai aka yi haka a bisa kuskure daga baya kuma aka fahimci kamfanin fasa duwatsun yana aki ne a karkashin dokokin Nijeriya na ‘Land Use Act of 1978, Sections 44 (3)’ na kundin tsarin mulkin Nijeriya na shekarar 1999 sashi na 1 na dokokin Albarkatun Kasa na Nijeriya na shekarar 2007.

A bisa dubi ga muhimmancin tsaro na kasa, kamfanin fasa duwatsun ya shirya barwa hukumar gidajen yarin wajen tare da komawa wani wajen daban amma suna neman lallai a biya su diyyar asarar harkokin kasuwanci da za su yi sakamakon asarra harkokin kasuwan ci da za su yi in har sun tashi daga inda aka san su.

Masu ruwa da tsaki a harkokin hakar ma’adanai sun sanya baki inda suka bukaci gwamnatin tarayya ta biya kamfanin fasa duwatsun diyyar asarar da za su yi sakamakoin mamaye wurin da hukumar Gidajen Yarin ta yi.

A ra’ayin wannan jaridar, duk da shirin gwamnatin Buhari na samar da gidajen yari na zamani da zai ka ga kawo karshen matsalolin da ake fuskanta a harkokin gudanar da gidajen yari a Nijeriya, yana kuma da matukar muhimmanci a warware dambarwar da ke tattare da kamfanin fasa duwatsu na Karshi don samar da fahimtar juna da kuma kawo karshen rashin jituwar da ake fuskanta don a tabbatar da yi wa kowa adalci.

Haka kuma lallai shirin samar da gidan yari na zamani wani hangen nesa ne mai matukar muhimmanci, mussamman ganin yin haka zai karfafa yadda ake gudanar da harkokin gidajen yarin kasar nan, amma kuma yana da matukar muhimmanci a tabbatar da yin haka bai cutar da wani ba a cikin masu ruwa da tsaki ciki har da kamfann fasa dutse da ake takaddama da shi a halin yanzu a yankjin Karshi.

Kamfann fasa dutsen, kamfani ne na zamani yana kuma dauke da kayan aiki na zamani, ana kiyasta cewa, shi ne na uku a fadin tarayyar kasar nan, masu zuba jari ‘yan kasa da abokan kasuwancinsu na kasashen waje ne suka kafa kamfanin tare da zuba jari na miliyoyin Nairori amma wannan dambarwar tana neman ta karya wanan kokari da wadannan masu kishin kasar suka yi.

Haka kuma ma’aikatan wannan kamfanin da a halin yanzu suka rasa ayyukansu duk ‘yan Nijeriya ne da wannnan rikicin ya sa suka rasa hanyar cin abincin su.

A matsayinmu na gidan jarida muna kira ga gwamnatin tarayya da ta yi a bin da ya kamata na biyan kamfanin diyyar da suka kamata tare da warware dukkan matsalolin da suka dabaibaye lamarin gaba daya a bisa lura da abin da ya shafi tsaron kasa da kuma hakki na kamfanin fasa dutsen.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kyawawan Dabi’u, Tausayi, Jinkai Da Rahamar Manzon Allah (SAW)

Next Post

Ba Za A Kara Tsawaita Wa’adin Daina Karbar Tsofaffin Takardun Kudi Ba —Emefiele

Related

Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba
Labarai

Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

4 hours ago
Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara
Labarai

Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

6 hours ago
2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe
Labarai

2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

8 hours ago
SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa
Labarai

SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

9 hours ago
DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci
Labarai

DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

10 hours ago
PDP Ta Dakatar Da Tsofaffin Ministoci 2 Da Wasu 5 Kan Yi Wa Jam’iyyar Zagon-Kasa
Labarai

PDP Ta Dakatar Da Shugabanta Na Kasa Kan Zargin Yi Wa Jam’iyyar Adawa Aiki

19 hours ago
Next Post
Ba Za A Kara Tsawaita Wa’adin Daina Karbar Tsofaffin Takardun Kudi Ba —Emefiele

Ba Za A Kara Tsawaita Wa'adin Daina Karbar Tsofaffin Takardun Kudi Ba —Emefiele

LABARAI MASU NASABA

Kafar CGTN Ta Gabatar Da Jerin Bidiyo Don Yin Bayani Game Da Tsarin Demokuradiyyar Kasar Sin

Kafar CGTN Ta Gabatar Da Jerin Bidiyo Don Yin Bayani Game Da Tsarin Demokuradiyyar Kasar Sin

March 27, 2023
Kafa Dangantakar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Honduras Ya Sake Tabbatar Da Manufar Sin Daya Tak A Duniya

Kafa Dangantakar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Honduras Ya Sake Tabbatar Da Manufar Sin Daya Tak A Duniya

March 27, 2023
Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

March 27, 2023
Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

March 27, 2023
2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

March 27, 2023
SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

March 27, 2023
DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

March 27, 2023
Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 3 A Wasu Birane

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 5

March 27, 2023
PDP Ta Dakatar Da Tsofaffin Ministoci 2 Da Wasu 5 Kan Yi Wa Jam’iyyar Zagon-Kasa

PDP Ta Dakatar Da Shugabanta Na Kasa Kan Zargin Yi Wa Jam’iyyar Adawa Aiki

March 26, 2023
Amurka Ta Sake Zargin Kasar Sin Kan Asalin Kwayar Cutar COVID-19 Domin Yunkurin Siyasa

Amurka Ta Sake Zargin Kasar Sin Kan Asalin Kwayar Cutar COVID-19 Domin Yunkurin Siyasa

March 26, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.