Da safiyar yau Alhamis 14 ga watan Mayun nan ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gana da tawagar ‘yan kasuwan Amurka da suka rako shugaba Trump a ziyarar da yake yi a kasar Sin. Shugaba Xi ya gana da ’yan kasuwar ne a babban zauren taruwar jama’a dake nan birnin Beijing.
Yayin ganawar, shugaba Trump ya bayyana cewa, a wannan ziyara tasa yana tare da fitattun wakilan ‘yan kasuwar Amurka, wadanda dukkaninsu ke mutunta, da darajanta kasar Sin. Ya kuma karfafa musu gwiwar fadada hadin gwiwa da Sin. Kazalika, Trump ya gabatar da ‘yan kasuwan da suka rako shi daya bayan daya ga shugaba Xi.
A nasu bangare. ’yan kasuwan na Amurka sun bayyana cewa, suna matukar darajanta kasuwar Sin, kuma suna fatan zurfafa ayyukansu a Sin, da kuma karfafa hadin gwiwa da Sin.
Shi kuwa shugaba Xi cewa ya yi, kamfanonin Amurka suna shiga a dama da su sosai a ayyukan kwaskwarima, da bude kofa da Sin ke aiwatarwa, kuma bangarorin biyu suna cin gajiya daga hakan. Ya ce kofar Sin a bude take, kuma kasar za ta ci gaba da budewa, kana bangaren Sin yana maraba da karfafa hadin gwiwa tsakanin Amurka da Sin, ya kuma yi imanin cewa, kamfanonin Amurka za su samu kyakkyawar makoma a Sin. (Amina Xu)















Discussion about this post