ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyakkyawar Huldar Manyan Kasashe Tushe Ne Na Bunkasuwar Duniya

by Sulaiman and CGTN Hausa
3 weeks ago
Kasa

Bisa gayyatar shugaban kasar Sin Xi Jinping, shugaban kasar Amurka Donald Trump na yin ziyarar aiki a kasar Sin daga ranar 13 zuwa 15 ga watan Mayu, ziyarar da ta kasance ta farko da shugaban kasar Amurka ya kawo wa kasar ta Sin cikin tsawon shekaru 9, kuma ganawarsu a wannan karo ta biyo bayan ganarwarsu a Busan a shekarar da ta gabata. Wannan ziyara ta ja hankalin duniya matuka, duba da cewa muhimmancinta ya riga ya wuce huldar da ke tsakanin kasashen biyu.

“Kyakkyawar dangantakar Sin da Amurka mai dorewa ta dace da muradun kasashen biyu, kuma fata ne na al’ummun duniya.” A ‘yan shekarun nan, shugaba Xi ya gabatar da jerin muhimman kalamai game da dangantakar Sin da Amurka, ya kuma yi cikakken bayani kan hanyar da ta dace tsakanin kasashen biyu a sabon zamani.

A ganawarsu ta yau 14 ga wata, shugaba Xi ya jaddada cewa, muradun bai daya tsakanin Sin da Amurka sun fi sabani a tsakaninsu, kuma nasarar kowannensu dama ce ga juna, kuma duniya za ta cin gajiyar kyakkyawar dangantakar Sin da Amurka. A bangarensa, shugaba Trump ya sha bayyana shugaba Xi a matsayin shugaba mai girma. Trump ya ce: “Ina alfahari da kasancewa abokinka, kuma alakar da ke tsakanin Sin da Amurka za ta ci gaba da inganta sama da lokutan baya.”

ADVERTISEMENT

Ingancin dangantakar Sin da Amurka yana shafar zaman lafiyar duniya. A matsayin kasashe biyu mafiya karfin tattalin arziki a duniya, jimillar tattalin arzikin Sin da na Amurka ta wuce kashi daya bisa uku na duniya baki daya, kuma jimillar cinikayyar kayayyaki a tsakaninsu ta kai kusan kashi daya cikin biyar na duniya. Ko a bara, kudin cinikayyar kasashen biyu ya kai kimanin dala biliyan 560, duk da takkadamar ciniki da suka fuskanta, adadin da ya yi daidai da jimillar tattalin arzikin wata kasa mai matsakaicin karfi a shekara guda.

A halin yanzu, yankin Gabas ta Tsakiya na ci gaba da fama da yake-yake, kuma matsalar zirga-zirgar jiragen ruwa ta mashigar Hormuz na kawo cikas ga tsaron makamashi na duniya, a yayin da ake fuskantar karin matsalolin tsaro wajen amfani da AI, kuma sauyin yanayi da sauran kalubalen duniya suna ta kunno kai. A cikin wannan yanayi mai sarkakiya, ganawar shugabannin Sin da Amurka ta aika da sako mai kyau ga duniya.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Al’ummun duniya suna fatan ganin ganawar shugabannin Sin da Amurka za ta taimaka ga fadada hadin gwiwarsu da kawar da matsalolin da ke tsakaninsu, tare da samar da kwanciyar hankali da tabbaci ga duniya mai fama da rashin tabbas. Kyakkyawar dangantakar Sin da Amurka ba kawai ta dace da muhimman muradun al’ummomin kasashen biyu ba, har ma ita ce fata na al’ummun duniya baki daya. Kazalika, taimakon juna tsakanin Sin da Amurka, ba wai kawai zai amfani kasashen biyu ba ne, har ma zai samar da alfanu ga duniya gaba daya.(Marubuciya: MINA)

Kasa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Kasa
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Kasa

Yadda Rashin Aikin Yi Ke Jefa Matasa Maula Da Bangar Siyasa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.