Da yammacin yau Laraba 13 ga watan Mayu agogon Beijing, shugaban Amurka Donald Trump ya iso birnin Beijing na kasar Sin ta jirgin sama.
Bisa gayyatar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi masa, shugaba Donald Trump na Amurka yana gudanar da ziyarar aiki a Sin daga ranar 13 zuwa 15 ga watan Mayu.
Wannan ita ce ganawa ta biyu ta ido-na-ganin ido tsakanin shugabannin kasashen Sin da Amurka bayan ganawarsu a Busan na Koriya ta Kudu a watan Oktoban bara, sannan kuma ita ce ziyarar farko da wani shugaban Amurka ya kawo Sin bayan shekaru tara.
Shugaba Xi Jinping zai yi musayar ra’ayoyi mai zurfi da shugaba Donald Trump kan manyan batutuwan da suka shafi dangantakar Sin da Amurka da kuma zaman lafiya da ci gaban duniya.
Mataimakin shugaban kasar Sin Han Zheng ne ya tarbe shi a filin saukar jiragen sama dake Beijing. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post