ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kwamitin AU: Ya Kamata Kasashe Masu Tasowa Su Gabatar Da Shirin Daidaita Tsarin Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
AU

A ranar Juma’a da ta gabata, shugaban kwamitin kungiyar tarayyar Afirka ta AU, Mahamoud Ali Youssouf, ya zanta da wakilin kafar CMG, a birnin Addis Ababa na kasar Habasha, ta wani shirin telabijin na musamman mai taken “Leaders Talk” da aka dauka, inda shugaban ya tabo batun kutsawa cikin kasar Venezuela, da sace shugaban kasar da uwargidansa, da sojojin kasar Amurka suka yi a kwanan baya.

Game da hakan, a cewar mista Mahamoud Youssouf, kungiyar AU ta yi kira ga kasashen duniya da su girmama ka’idojin kasa da kasa. Ban da haka, ya ce ya kamata kasashe masu tasowa su fara daukar matakai, domin gabatar da wani shiri na maye gurbin tsoffin tsare-tsaren duniya, wadanda ke bakin rushewa.

Mista Mahamoud Youssouf ya ce, lamarin da ya abku a kasar Venezuela, a ganin dimbin manazarta al’amuran duniya, tamkar matakin karshen ne na kawo karshen tsare-tsaren duniya na yanzu. Duk da haka, Mista Youssouf ya ce yana tafe da hasashe mai yakini, na fatan ganin wani sabon tsarin da zai maye gurbin tsoffin tsare-tsaren duniya dake rugujewa, kuma yana fatan ganin kasashen Afirka da kasar Sin, tare da sauran kasashe masu tasowa, sun gabatar da wani sabon tsarin kula da al’amuran duniya bisa hadin gwiwarsu.

ADVERTISEMENT

Ban da haka, Mista Youssouf ya kara da cewa, ya kamata a girmama ka’idojin kasa da kasa, da tsarin gudanar da harkokin duniya. Saboda haka kungiyar tarayyar Afirka ta AU, sam ba ta amince da matakin tsare shugaban wata kasa ba. Kana kungiyar ta riga ta gabatar da wata sanarwa mai bayyana ra’ayinta a fili, inda ta bukaci kasar da lamarin ya shafa, da ta girmama dokokin kasa da kasa, da kariyar da aka baiwa shugabannin kasashe daban daban daga tuhumar aikata laifi.

Dangane da manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, Mista Mahamoud Youssouf ya ce, AU ta yarda, gami da tsayawa kan manufar, saboda a ganinsa, iyakokin kasar Sin na da matsayi mai matukar muhimmanci iri daya da na kasashen Afirka. Ya kara da cewa, yunkurin balle Somaliland daga kasar Somaliya da ake fuskantar a nahiyar Afirka, ya shaida bukatar kokarin dakile ra’ayin janyo baraka ga wata kasa, saboda haka, matakin kasashen Afirka na tsayawa kan manufar Sin daya taka a duniya, tamkar taimakon kansu ne ta fuskar kare hurumin yankunan kasa. Wannan dalili, a cewar mista Youssouf, ya sa kasashen Afirka ke tsayawa tare da kasar Sin a ko da yaushe, kan batun nan na kasancewar Sin daya tak a duniya. (Bello Wang)

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

 

 

AU
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
AU
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Amsa Wasikar Malamai Da Dalibai Na Tawagar Mu’amalar Matasa Ta Amurka

Xi Jinping Ya Amsa Wasikar Malamai Da Dalibai Na Tawagar Mu’amalar Matasa Ta Amurka

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.