Kasar Sin ta dauki matakin soke harajin kwastam ga kayayyakin kasashen Afirka masu huldar diflomasiyya da ita, lamarin da ya jawo tofa albarkacin baki da sam-barka a kasashe daban-daban na nahiyar.
A yayin da yake tattaunawa da wakilin CMG, shugaban kasar Saliyo, Julius Maada Bio, ya ce kasar Sin babbar kasuwa ce, kuma tana kokarin samun ci gaba tare da Afirka bisa wannan matakin na soke haraji.
Shugaba Bio ya kara da cewa, kasar Sin ta bayyana karara cewa tana bai wa kasashen Afirka da ke da huldar diflomasiyya da ita damar fitar da kayayyaki zuwa gare ta ba tare da biyan haraji ba, wanda ya nuna ainihin kyakkyawar dangantakar dake tsakaninmu, kana matukar an cika ka’idoji, za a iya shiga wannan babbar kasuwa.
Ya kara da cewa, abin da muke fatan gani shi ne, samun wata kasar Sin dake neman ci gaba tare da abokanta. Kuma ci gaba da abota ba sa cin karo da juna.
Kazalika, yayin da kasar Sin take cimma nata ci gaban, kasar tana kuma son neman ci gaba tare da abokanta, wanda hakan zai sa duniya ta kara samun zaman lafiya. (Bilkisu Xin)















Discussion about this post