ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya

by Leadership Hausa
19 seconds ago
Taba

Majalisar Dinkin Duniya ce, ta ayyana duk ranar 31 na watan Mayun ko wacce shekara, a matsayin ranar yaki da shan Taba Sigari.

Taken taron na 2026 wanda ta kaddamr shi ne, “Dakile Sanadarin Cikin Sigari Da Ke Sanya Mutum Ya Dawwama Yana Shaye Shaye wato a turance Nicotine da kuma zukar ita kanta Tabar Sigari”.

Wannan taken dai, ya zo kan gaba a kasar nan duba da yadda ake ci gaba da samun, karuwar masu shanta, ciki har da wasu yaran kasar.

ADVERTISEMENT

A nan, ba wai ana nunfin Nijeriya ta gaza yakar dabi’ar bane, sai kawai, yadda ake kara samun yawan wasu shaguna a kasar, da ake sayar da ita, tamkar ana sayar da Biskit ko Alawa.

Abin dubi a nan shi ne, yadda wasu matasan kasar, suka rungumi dabi’ar, babu kakkautawa, musamman duba da cewa,  akalla matasan kasar, daga tsakanin kaso hudu zuwa kaso 5.6 ko akalla zuwa kaso bakwai zuwa sha daya, na yin dabi’ar

LABARAI MASU NASABA

Afirka Ta Kudu Ta Kafa Mummunan Tarihi A Gasar Kofin Duniya

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

Wannan adadin idan aka kwatanta, bai na yawan sauran matasa a duniya, da ke yin dabi’ar ba.

Bisa wasu alkaluma da Hukumar Kula da Dakile Shan Taba Sigari ta Kasa wato NTCA ta fitar a kwanan baya, sun nuna cewa, a kasar nan, a duk yara dalibai biyar masu shekaru daga tsakanin 13 zuwa 15, ana samun daya, da ke zukar Taba Sigari

Kazalika, a duk cikin yaran goma, akawi daya sun yi nisa, a yin dabi’ar.

Wasu alkaluma sun bayyana cewa, a duk shekara, akalla ‘yan Nijeriya 30,000 ke utuwa, saboda kamuwa da cutkan da suka shafi yin tu’ammli da shan Sigari, musamman kansar Huhu.

A gafe daya kuma, wadanda suka kamu da cutukan, a duk shekara, na kashe akalla Naira biliyan 211.2, wajen duba lafiyarsu.

Bugu da kari, matsalar na kuma sanya wa, Nijeriya na yin rashin matasa, maso tasowa, saboda kamuwa da cutuakan, da ke da alaka, da shan Taba Sigari.

Nijeriya ba wai ta kasance, Kara zube bane, wajen samar dokoki, musamman  na dakile yin dab’ar ba, domin kuwa, an kirkiri, da Hukumar  Kula da Dakile Shan Taba Sigari ta Kasa,  inda kuma kasar, ta kasance, tana daga cikin kasashen, da suka rattaba hannun yarjejeniya Hukumar Kula da Lafiya ta Duniya, kan dakile yin dabi’ar

Wannan Jaridar, a bayyane,  matsalar da ke son bajewa a Faifai shi ne, batun samar da dokar dakile dabi’ar, da kuma batun tsarara,  wanzar da matakan  dakile ta.

Alamu na nuna cewa, ba wai kadai dogara kan dokar hana bayar da tallan Sigarin a kafafe ko kuma bin ka’ido ne, batun ba, amma rashin nuna da gasken da ake yi, na wanzar da dokar yadda za ta yi tasiri a kasar, shi ne babban kalubalen.

Haka zalika, batun iya sayen Sigari ta kafar Yanar Gizo da aka kirkro a kasar, hakan ya sanya, ana ci gaba da samun wawagegen gibi, na wanzar da dokar a kasar, yadda ta kamata.

Muna kira ga Ma’aikatar Kiwon Lafiya ta Tarayya da Hukumar  Kula da Dakile Shan Taba Sigari ta Kasa NTCA da kuma Hukumar Kula da Abinci da Magunguna ta Kasa wato NAFDAC, da su kara kaimi, wajen daukar matakan da suka kamata, domin a rage matsalar.

Ya zama wajbi, Gwamnati ta tashi tsaye haukan, domin dakile yin amfani da kuma sayar da duk wata na’uin Taba Sigari, musamman wadda masana’an suka sarrafa, da sanadaran da ke sanya dandano.

Bugu da kari ya zama wajibi, gwamnatin ta kara tsaurara matakai, kan tallan Taba Sigari a kafafen tallace-tallace, musamman domin a ceto rayuwar yaran kasar, wadanda sune, manyan gobe.

Akwai matukar bukatar, mahukunta a kasar, su tabbatar da sun kara jabga haraji kan masana’antun da ke sarrafa Sigari.

Kazalika, akwai bukatar duba lafiyar matasan kasar, da suka rungumi, wannan dabi’ar.

A nan, muna jinjinawa kungiya ta da ke yaki da shan Taba Sigari ta kasa wato NCS bisa kirkiro da kungiyar matasa da ke yin gangamin wayar da kai, kan illolin dabi’ar.Wannan salon, zai taimaka wajen wayar da kan matasan kasar da suka rungumi dabi’ar, yin watsi, da ita.

Akwai kuma matukar bukatar, yin hadaka da Gwamnati tare da zuba kudade a cikin shirye-shiyen kiwon lafiya.

A duk shekara, wasu masna’antu a kasar nan, na sarrafa wasu kaya masu lahani, da ke shafar lafiyar dubban matasan kasar.

Hakan ba wai, batu ne, na harkar kasuwanci ba, amma wani tsari ne, da aka kitsa a zamanance, domin tarwatsa rayuwar matasan.

Abin takaicin shi ne, rashin mayar da hankali a bangaren masu rike da madafun iko na siyasa, domin a dakile dabi’ar a kasar baki daya.

Muna kira ga Gwamnatin kasar da ta dauki matakan gaggawa, domin tsamo, musamman matasan kasar nan, daga cikin matsalar.

Taba
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe

MASU ALAKA

Afirka Ta Kudu Ta Kafa Mummunan Tarihi A Gasar Kofin Duniya
Manyan Labarai

Afirka Ta Kudu Ta Kafa Mummunan Tarihi A Gasar Kofin Duniya

June 11, 2026
Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

June 11, 2026
Majalisa Ta Amince Da Ƙudirin Dokar Kafa ‘Yansandan Jihohi.
Manyan Labarai

Majalisa Ta Amince Da Ƙudirin Dokar Kafa ‘Yansandan Jihohi.

June 11, 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya

Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya

June 12, 2026
Sin Ta Fitar Da “Shirin Aiki Na Kasa Kan Hakkin Dan Adam Na (2026-2030)”  

Sin Ta Fitar Da “Shirin Aiki Na Kasa Kan Hakkin Dan Adam Na (2026-2030)”  

June 11, 2026
Afirka Ta Kudu Ta Kafa Mummunan Tarihi A Gasar Kofin Duniya

Afirka Ta Kudu Ta Kafa Mummunan Tarihi A Gasar Kofin Duniya

June 11, 2026
Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya

Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya

June 11, 2026
Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar

Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar

June 11, 2026
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Matsalar Tsaro: Manoma Sun Koma Gonakinsu A Katsina – Dikko Radda

June 11, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama

Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama

June 11, 2026
Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa

Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa

June 11, 2026
An Rufe Makarantu A Mexico Saboda Fara Gasar Kofin Duniya

An Rufe Makarantu A Mexico Saboda Fara Gasar Kofin Duniya

June 11, 2026
An Kaddamar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Dan Adam Na Shekarar 2026 A Beijing

An Kaddamar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Dan Adam Na Shekarar 2026 A Beijing

June 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.