Majalisar Dinkin Duniya ce, ta ayyana duk ranar 31 na watan Mayun ko wacce shekara, a matsayin ranar yaki da shan Taba Sigari.
Taken taron na 2026 wanda ta kaddamr shi ne, “Dakile Sanadarin Cikin Sigari Da Ke Sanya Mutum Ya Dawwama Yana Shaye Shaye wato a turance Nicotine da kuma zukar ita kanta Tabar Sigari”.
Wannan taken dai, ya zo kan gaba a kasar nan duba da yadda ake ci gaba da samun, karuwar masu shanta, ciki har da wasu yaran kasar.
A nan, ba wai ana nunfin Nijeriya ta gaza yakar dabi’ar bane, sai kawai, yadda ake kara samun yawan wasu shaguna a kasar, da ake sayar da ita, tamkar ana sayar da Biskit ko Alawa.
Abin dubi a nan shi ne, yadda wasu matasan kasar, suka rungumi dabi’ar, babu kakkautawa, musamman duba da cewa, akalla matasan kasar, daga tsakanin kaso hudu zuwa kaso 5.6 ko akalla zuwa kaso bakwai zuwa sha daya, na yin dabi’ar
Wannan adadin idan aka kwatanta, bai na yawan sauran matasa a duniya, da ke yin dabi’ar ba.
Bisa wasu alkaluma da Hukumar Kula da Dakile Shan Taba Sigari ta Kasa wato NTCA ta fitar a kwanan baya, sun nuna cewa, a kasar nan, a duk yara dalibai biyar masu shekaru daga tsakanin 13 zuwa 15, ana samun daya, da ke zukar Taba Sigari
Kazalika, a duk cikin yaran goma, akawi daya sun yi nisa, a yin dabi’ar.
Wasu alkaluma sun bayyana cewa, a duk shekara, akalla ‘yan Nijeriya 30,000 ke utuwa, saboda kamuwa da cutkan da suka shafi yin tu’ammli da shan Sigari, musamman kansar Huhu.
A gafe daya kuma, wadanda suka kamu da cutukan, a duk shekara, na kashe akalla Naira biliyan 211.2, wajen duba lafiyarsu.
Bugu da kari, matsalar na kuma sanya wa, Nijeriya na yin rashin matasa, maso tasowa, saboda kamuwa da cutuakan, da ke da alaka, da shan Taba Sigari.
Nijeriya ba wai ta kasance, Kara zube bane, wajen samar dokoki, musamman na dakile yin dab’ar ba, domin kuwa, an kirkiri, da Hukumar Kula da Dakile Shan Taba Sigari ta Kasa, inda kuma kasar, ta kasance, tana daga cikin kasashen, da suka rattaba hannun yarjejeniya Hukumar Kula da Lafiya ta Duniya, kan dakile yin dabi’ar
Wannan Jaridar, a bayyane, matsalar da ke son bajewa a Faifai shi ne, batun samar da dokar dakile dabi’ar, da kuma batun tsarara, wanzar da matakan dakile ta.
Alamu na nuna cewa, ba wai kadai dogara kan dokar hana bayar da tallan Sigarin a kafafe ko kuma bin ka’ido ne, batun ba, amma rashin nuna da gasken da ake yi, na wanzar da dokar yadda za ta yi tasiri a kasar, shi ne babban kalubalen.
Haka zalika, batun iya sayen Sigari ta kafar Yanar Gizo da aka kirkro a kasar, hakan ya sanya, ana ci gaba da samun wawagegen gibi, na wanzar da dokar a kasar, yadda ta kamata.
Muna kira ga Ma’aikatar Kiwon Lafiya ta Tarayya da Hukumar Kula da Dakile Shan Taba Sigari ta Kasa NTCA da kuma Hukumar Kula da Abinci da Magunguna ta Kasa wato NAFDAC, da su kara kaimi, wajen daukar matakan da suka kamata, domin a rage matsalar.
Ya zama wajbi, Gwamnati ta tashi tsaye haukan, domin dakile yin amfani da kuma sayar da duk wata na’uin Taba Sigari, musamman wadda masana’an suka sarrafa, da sanadaran da ke sanya dandano.
Bugu da kari ya zama wajibi, gwamnatin ta kara tsaurara matakai, kan tallan Taba Sigari a kafafen tallace-tallace, musamman domin a ceto rayuwar yaran kasar, wadanda sune, manyan gobe.
Akwai matukar bukatar, mahukunta a kasar, su tabbatar da sun kara jabga haraji kan masana’antun da ke sarrafa Sigari.
Kazalika, akwai bukatar duba lafiyar matasan kasar, da suka rungumi, wannan dabi’ar.
A nan, muna jinjinawa kungiya ta da ke yaki da shan Taba Sigari ta kasa wato NCS bisa kirkiro da kungiyar matasa da ke yin gangamin wayar da kai, kan illolin dabi’ar.Wannan salon, zai taimaka wajen wayar da kan matasan kasar da suka rungumi dabi’ar, yin watsi, da ita.
Akwai kuma matukar bukatar, yin hadaka da Gwamnati tare da zuba kudade a cikin shirye-shiyen kiwon lafiya.
A duk shekara, wasu masna’antu a kasar nan, na sarrafa wasu kaya masu lahani, da ke shafar lafiyar dubban matasan kasar.
Hakan ba wai, batu ne, na harkar kasuwanci ba, amma wani tsari ne, da aka kitsa a zamanance, domin tarwatsa rayuwar matasan.
Abin takaicin shi ne, rashin mayar da hankali a bangaren masu rike da madafun iko na siyasa, domin a dakile dabi’ar a kasar baki daya.
Muna kira ga Gwamnatin kasar da ta dauki matakan gaggawa, domin tsamo, musamman matasan kasar nan, daga cikin matsalar.














Discussion about this post