Shekaru aru-aru, inji Bahaushe, yara a kasar na gudanar da shagulgulan binkin zagayowar ranarsu ta duniya, musamman a cikin walwala da annashawa.
An dai gudanar da bikin zagayowar ranar ce, a duk ranar 27, na kowanne watan Mayu na shekara, tare da fatan samun makomar gobe mai kyau, yaran manyan gobe.
Sai dai, abin takaicin, bisa lamuran da ke bijirowa, a duniya ta yau, za a iya ce, wannan burin na yaran, da kamar wuya.
Su ma yara a Nijeriya, ba a bar su a baya, wajen murnar bikin zagoyowar ranar ba, wadda 2026, aka yi mata take da, “ Moma ayau: Janyo Yaran Kasar Nan A Jiki Domin Inganta Makomarsu,”.
Abin bakin cikin a nan shi ne, miliyoyin yara a kasar nan fatan inganta samar masu makomar ta gari, na ci gaba da zama rashin tabbas, musamman duba da yadda suke ci gaba da zama, a cikin tsabagen yunwa, fargaba, cin zarafinsu, nuna masu wariya, zama a cikin duhun jahilci, fusknatar tashin hankula, yin watsi da rayuwarsu.
A saboda wadannan jerin kalubalen da muka jero, muke ganin, har yanzu, akwai sauran Rina a Kaba, a makomar yara, a Nijeriya.
Kazalika, har yanzu, kasar, ba ta daura damarar samar da kyakywan yanayi, ga makomar yaran kasar, da kuma sauran yaran da ke tafe, a nan gaba ba.
A yayin da jami’an gwamnati ke tunkahon cewa, an samar da shirye-shiryen janyo yaran a jiki, amma a bayan fage, alkaluma na nuna yadda rayuwar yaran, ke ci gaba da fusknatar, dimbin matsaloli.
Bisa yawan yaran da ake da su, a fadin duniya, yara a Nijeriya, su ne, mafi koma baya, da rayuwarsu, ke ci gaba da zamowa, a cikin hatsari.
Karin wata matsalar ita ce, yadda fannin ilimin Bokon kasar, ke ci gaba da tabarbarewa, musamman duba da cewa, an kiyasa, yara miliyan 18.3 ne, suka daina zuwa makaranta, inda wannan adadin, ya rubanya na fadin duniya.
Hakan na nuna cewa, a duk cikin yara biyar, yaro daya, bai zuwa makaranta.
Daga cikin wannan adadin, kimanin yara, kaso 66 da suka daina zuwa makaranta na a yankunun Arewa Maso Gabas da kuma Arewa Maso Yamma, da kalubalen rashin tsaro, ke ci gaba da ta’azzara, musamman na ayyukan ‘yan bindiga, ‘yan fashin daji da kuma yadda hare-hare, ya tarwatsu, daga matsugunansu.
Haka zalika, saboda kalubalen rashin tsaro, an rufe makarantu da dama, tare da kai hare-hare, tare da mayar da Azuwa, Fagan fama.
Fannin na ilimin, ya kara tagaiyara, bayan sace dalibai mata, sama da 1,700, ‘yan makarantar Chibok a 2014, inda hakan ya nuna, babbar koma baya, ga ci gaban rayuwar yara.
Misali, a ranar 15 na watan Mayun 2026, wasu ‘yan bindiga, suka kutsa wasu makarantun Firamare da Sakandare da ke a yankin Esiele da Yawota a karamar hukumar Oriire a jihar Oyo, suka sace dalibai da malamai.
Miliyoyin yara a kasar, na fuskantar kalubalen rashin abinci mai gina jiki, inda kuma kimain miliyan 11, ke ci gaba da fuskantar matsananciyar yunwa, musamman yadda yara kaso 32, ‘yan kasa da shekaru biyar, suma ke ci gaba da fuskantar matsalar.
A gafe daya kuma, ba a tanadi wani kyajyawan tasri, a fannin kiwon lafiya ba, wanda hakan, ke ci gaba da janyo, mutuwar yaran, musamman duba da yadda, a duk haiwa daya, ake samun yara daga 115 zuwa 128 ke rasuwa, kafin cikarsu bikin ranar haihuwarsu.
Yaran na kuma mutuwa saboda cizon Sauro da kwalara da Amai da gudawa, wadanda za a iya magancewa, a cikin gaggawa.
Kimain alumomi sama da miliyan 3.7, ciki har da yara, da mata a daukacin fadin kasar, ke gudun hijira, inda adadin yaran, ya kai kaso 70.
Wannan matsalar ta shafi neman iliminsu da rashin samun kulawar lafiyarsu da kuma rashin samun abinci mai gina jiki.
Kazalika, akwai kuma yaran da ake tilastawa yin ayyukan bauta, duba da alkaluman da Hukumar Kiddidiga ta kasa ta fitar, sun nuna yaran da ke yin aikin bautar sun kai kimanin, miliyan 24.67.
Irin wadannan yara, shekarun na faraway ne, daga biyar zuwa 17, inda sama da miliyan 14, ake tilasta su yin aikin bauta, masu hatsari, wanda hakan, ke shafar lafiyarsu da kuma tunaninsu
Matsain tattalin arzki da iyayen irin wadannan yaran ke fama da shi, hakan ya sanya, suna tura ‘ya’yansu, yin tallace-tallace, hakar ma’adanai, ta haramtacciyar hanya.
Ya zama wajibi a kasar, bkin zagowar ranar, ta wuce batun gabatar da kasidu, amma a dauki kwararan matakai, domin intanta rayuwar yaran
Dole ne kuma, matakan gwamnati uku na kasar, su tabbatar da sun wanzar da dokar, bai wa yara ‘yancinsu, da kuma karfafa dokar kare cin zarafinsu da yiwa ‘ya’ya mata auren wure da safarar yara da kuma sanya su, yin aikin bauta.
Bugu da kari, ya zama wajibi, hukumomin tsaro da bangaren Shari’a, su tabbatar da ana hukunta duk wanda aka samu, da cin zarafin yaran.
Haka zalika, ya zama wajbi, gwamnati ta ayyana dokar ta baci, a fannin ilimi, musamman, a yankunan da rashin tsaro, ya daidaita tare da sake gina makarantun da hare-haren ‘yan ta’adda, suka lalata.
Dole ne, kuma a farfado da cibiyoyin kiwon lafiya da ke a karkara tare da mayar da hankali wajen samar da shirye-shiryen samar da abinci mai gina jiki, musamman ga masu juna biyu da kananan yara.
Dole ne, taken taron bikin na bana, ya zama a aikace, wajen samar da tsaro a makarantu da samar da ingantattun kayan duba lafiya da samar da abinci mai gina jiki da samar da ingantacce kuma tsaftattacen ruwa sha da dakile yawan, aukuwar tashe-tashen hankula, a cikin alumomin kasar.















Discussion about this post