Ma’aikatar tsaron kasar Sin ta sanar a yau Talata cewa, dakarun sojin ruwa na kasar da na Indonesiya za su gudanar da atisayen kewaya teku a yankin ruwan da ke gabashin tsibirin Taiwan na kasar Sin a tsakiyar watan Agustan nan.
Ma’aikatar tsaron ta kuma bayyana cewa, wannan atisaye na da nufin inganta karfin gudanar da ayyuka na hadin gwiwa a tsakanin dakarun sojin ruwan guda biyu ne, da zurfafa hadin gwiwa a aikace, gami da kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a shiyyar. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
ADVERTISEMENT














