Ma’aikatar kula da cinikayya ta kasar Sin ta gabatar da hukunci na wucin gadi dangane da binciken da take yi kan gyadar pecan da ake shigarwa kasar daga kasashen Mexico da Amurka, inda ta gano cewa, ana jibge su a kasuwar kasar Sin cikin farashin da ya yi kasa sosai da wanda ake sayarwa a kasashensu na asali, lamarin da ke illa ga masu samar da ita a cikin gidan kasar Sin.
An fara gudanar da binciken ne a ranar 25 ga watan Satumban 2025. ma’aikatar ta ce ta yi amfani da dokokin yaki da jibge kayayyaki na kasar Sin da ka’idojin hukumar kula da cinikayya ta duniya (WTO), kuma ta tabbatar da adalci da rashin nuna bangaranci da tsare gaskiya, kuma ba tare da rufa-rufa ba.Ta ce ta yanke shawarar daukar matakan wucin gadi na yaki da jibge kayayyaki.
Inda ta yanke hukuncin ayyana kaso 17.8 zuwa kaso 51.6 a matsayin harajin da kamfanonin Mexico za su biya. Kana bisa la’akari da rashin shigar kamfanonin Amurka cikin binciken, ta ayyana kaso 54.3 a matsayin haraji ga dukkan kamfanonin amurka, tana cewa ta yi hakan ne bisa dokokin kasar Sin da ka’idojin WTO.
A cewar ma’aikatar, kasar Sin za ta ci gaba da gudanar da bincike bisa doron doka, da kare halaltattun hakkokin dukkan masu ruwa da tsaki, tare da tabbatar da adalci wajen yanke hukunci na karshe, bisa la’akari da sakamakon binciken. (Fa’iza Mustapha)














