• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Ba Da Gudunmawar Ci Gaban Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Na Ba Da Gudunmawar Ci Gaban Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abokai, yayin da ‘yan kwanaki suka rage a fara gasar cin kofin kwallon kafan duniya ta hukumar FIFA ta 2022 a Qatar, yau “duniya a zanen MINA” zai bayyana muku abubuwan dake da alaka da kasar Sin a wannan gasa da ma duniya.

Yayin da ka yi yawo a wajen filin wasa na Al Bayt , abin da zai shakatar da kai a filin, shi ne wasu bishiyoyi masu kyaun gani na kudancin kasar Sin da yawansu ya kai fiye da dubu 50, da kamfanin samar da tsirrai na birnin Foshan na lardin Guangdong dake kudancin Sin ya yi jigilarsu zuwa wurin.

  • Masana: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Karfin Afirka A Fannin Aikin Injiniya

Ban da wannan kuma, sama da kashi 50% na kayayyakin dake da alaka da gasar daga birnin Yiwu na Sin ne aka samar, baya ga rigunan wasa na fitattun kungiyoyin ‘yan wasa na kasashe 32 da mai tsara salon tufa na Sin ya gabatar da mutum zai iya saya.

Haka kuma, kamfanin Sin ne ya gina filin wasa na Lusail, daya daga cikin filaye mafiya kayatarwa da muhimmanci na gasar.
Bayan ga wadannan abubuwa da Sin ta samar a gasar, yanzu haka kayayyakin da Sin ta samar da manyan ababen more rayuwa da Sin ta gina sun karade sassa na duniya. Idan muka juya ga nahiyar Afrika kuwa, daga layin dogo tsakanin Tanzaniya da Zambiya zuwa layin dogo dake tsakanin Abuja da Kaduna, daga madatsar ruwa ta Merowe zuwa tashar jirgin ruwa mai zurfi ta Lekki ta ciniki cikin ‘yanci, da ma wasu abubuwa na yau da kullum, dukkansu Sin ce ta gina su.

Tambayar ita ce, wai me ya sa kasar Sin ta gina wadannan abubuwa masu tarin yawa a duniya?
Bayan shekaru fiye da 40 da Sin ta fara aiwatar da manufar yin kwaskwarima a gida da bude kofa ga waje, Sin ta zama kasa mai karfi a fannin masana’antu a duniya. Ban da wannan kuma, a cikin tsarin zamanintar da masana’antu da Sin ta gudanar, gwamnati ta mai da hankali matuka kan kimiyya da fasaha.

Labarai Masu Nasaba

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

Kayan Aro Baya Rufe Katara

Alal misali, layin dogo da kamfanin Sin ya shimfida a cikin Abuja, shi ne irinsa na farko a yammancin Afrika dake amfani da tsarin kasar Sin. Ban da wannan kuma, fasahar sadarwa ta 5G da manyan ababen dangane da hakan da ake amfani da su yanzu a Afrika, su ma kamfanonin Sin suka gina su.

Sanin kowa ne cewa, ana yabawa kayayyakin da Sin ta samar saboda inganci da kuma araha, baya ga haka, abubuwan da Sin ta samar ta hanyar kirkire-kirkire bisa fasaha da kimiyya, sun fara jawo hankalin duniya.

Kasashe daban-daban na sa ran shigo da kayayyakin Sin cikin kasashensu da kuma hada kai da kamfanonin Sin a fannin samar da kayayyaki da fasaha da kimiyya, kazalika suna zabar kamfanonin Sin, don su taimaka musu wajen gina wasu manyan ababen more rayuwa.

A nata bangare, Sin tana matukar fari ciki wajen hada kai da kasashen duniya musamman ma kasashe masu tasowa don samun moriya tare.(Mai zane da rubuta:MINA)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 29 Da Cafke Masu Taimaka Musu 10 Da Naira Miliyan 15

Next Post

Peng Liyuan Ta Gana Da Uwar Gidan Shugaban Indonesia

Related

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

14 hours ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Daga Birnin Sin

Kayan Aro Baya Rufe Katara

15 hours ago
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

16 hours ago
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 
Daga Birnin Sin

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

17 hours ago
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

18 hours ago
Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa

19 hours ago
Next Post
Peng Liyuan Ta Gana Da Uwar Gidan Shugaban Indonesia

Peng Liyuan Ta Gana Da Uwar Gidan Shugaban Indonesia

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

July 2, 2025
Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

July 2, 2025
David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

July 2, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutum 6 A Ƙauyukan Filato, Sun Jikkata Wasu

Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

July 2, 2025
An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.